< Farawa 19 >

1 Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And two of the messengers come toward Sodom at evening, and Lot is sitting at the gate of Sodom, and Lot sees, and rises to meet them, and bows himself—face to the earth,
2 Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
and he says, “Now behold, my lords, please turn aside to the house of your servant, and lodge, and wash your feet—then you have risen early and gone on your way”; and they say, “No, but we lodge in the broad place.”
3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
And he presses on them greatly, and they turn aside to him, and come into his house; and he makes a banquet for them, and has baked unleavened things; and they eat.
4 Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
Before they lie down, the men of the city—men of Sodom—have surrounded the house, from young even to aged, all the people from the extremity;
5 Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
and they call to Lot and say to him, “Where [are] the men who have come to you tonight? Bring them out to us, and we know them.”
6 Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
And Lot goes out to them, to the opening, and the door has shut behind him,
7 ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
and says, “Please, my brothers, do not do evil;
8 Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
now behold, I have two daughters who have not known anyone; please let me bring them out to you, and do to them as [is] good in your eyes; only do nothing to these men, for therefore they have come in within the shadow of my roof.”
9 Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
And they say, “Come near here”; they also say, “This one has come to sojourn, and he certainly judges! Now, we do evil to you more than [to] them”; and they press against the man, against Lot greatly, and come near to break the door.
10 Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
And the men put forth their hand, and bring in Lot to them, into the house, and have shut the door;
11 Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
and the men who [are] at the opening of the house they have struck with blindness, from small even to great, and they weary themselves to find the opening.
12 Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
And the men say to Lot, “Whom have you here still? Son-in-law, your sons also, and your daughters, and all whom you have in the city, bring out from this place;
13 gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
for we are destroying this place, for their cry has been great [before] the face of YHWH, and YHWH does send us to destroy it.”
14 Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
And Lot goes out and speaks to his sons-in-law, those taking his daughters, and says, “Rise, go out from this place, for YHWH is destroying the city”; and he is as [one] mocking in the eyes of his sons-in-law.
15 Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
And when the dawn has ascended, then the messengers press on Lot, saying, “Rise, take your wife, and your two daughters who are found present, lest you are consumed in the iniquity of the city.”
16 Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
And he lingers, and the men lay hold on his hand, and on the hand of his wife, and on the hand of his two daughters, through the mercy of YHWH to him, and they bring him out, and cause him to rest outside the city.
17 Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
And it comes to pass, when he has brought them outside, that he says, “Escape for your life; do not look behind you, nor stand in all the circuit; escape to the mountain, lest you are consumed.”
18 Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
And Lot says to them, “Oh not [so], my lord;
19 Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
now behold, your servant has found grace in your eyes, and you make great your kindness which you have done with me by saving my life, and I am unable to escape to the mountain, lest the evil cleave [to] me and I have died;
20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
now behold, this city [is] near to flee there, and it [is] little; please let me escape there (is it not little?) that my soul may live.”
21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
And he says to him, “Behold, I have also accepted your face for this thing, without overthrowing the city [for] which you have spoken;
22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
hurry, escape there, for I am not able to do anything until your entering there”; therefore he calls the name of the city Zoar.
23 A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
The sun has gone out on the earth, and Lot has entered into Zoar,
24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
and YHWH has rained on Sodom and on Gomorrah brimstone and fire from YHWH, from the heavens;
25 Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
and He overthrows these cities, and all the circuit, and all the inhabitants of the cities, and that which is shooting up from the ground.
26 Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
And his wife looks from behind him, and she becomes a pillar of salt!
27 Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
And Abraham rises early in the morning to the place where he has stood [before] the face of YHWH;
28 Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
and he looks on the face of Sodom and Gomorrah, and on all the face of the land of the circuit, and sees, and behold, the smoke of the land went up as smoke of the furnace.
29 Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
And it comes to pass, in God’s destroying the cities of the circuit, that God remembers Abraham, and sends Lot out of the midst of the overthrow in the overthrowing of the cities in which Lot dwelt.
30 Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
And Lot goes up out of Zoar, and dwells in the mountain, and his two daughters with him, for he has been afraid of dwelling in Zoar, and he dwells in a cave, he and his two daughters.
31 Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
And the firstborn says to the younger, “Our father [is] old, and there is not a man in the earth to come in to us, as [is] the way of all the earth;
32 Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
come, we cause our father to drink wine, and lie with him, and preserve a seed from our father.”
33 A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
And they cause their father to drink wine on that night; and the firstborn goes in and lies with her father, and he has not known in her lying down or in her rising up.
34 Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
And it comes to pass, on the next day, that the firstborn says to the younger, “Behold, I have lain with my father last night: we also cause him to drink wine tonight, then go in, lie with him, and we preserve a seed from our father.”
35 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
And they cause their father to drink wine on that night also, and the younger rises and lies with him, and he has not known in her lying down or in her rising up.
36 Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
And the two daughters of Lot conceive from their father,
37 ’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
and the firstborn bears a son and calls his name Moab: he [is] father of Moab to this day.
38 ’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.
As for the younger, she has also born a son and calls his name Ben-Ammi: he [is] father of the sons of Ammon to this day.

< Farawa 19 >