< Farawa 19 >

1 Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
And there came two angels to Sodom at even; and Lot sat in the gate of Sodom: and Lot seeing them rose up to meet them; and he bowed himself with his face toward the ground;
2 Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
And he said, Behold now, my lords, turn in, I pray you, into your servant’s house, and tarry all night, and wash your feet, and you shall rise up early, and go on your ways. And they said, No; but we will abide in the street all night.
3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
And he pressed on them greatly; and they turned in to him, and entered into his house; and he made them a feast, and did bake unleavened bread, and they did eat.
4 Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
But before they lay down, the men of the city, even the men of Sodom, compassed the house round, both old and young, all the people from every quarter:
5 Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
And they called to Lot, and said to him, Where are the men which came in to you this night? bring them out to us, that we may know them.
6 Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
And Lot went out at the door to them, and shut the door after him,
7 ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
And said, I pray you, brothers, do not so wickedly.
8 Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
Behold now, I have two daughters which have not known man; let me, I pray you, bring them out to you, and do you to them as is good in your eyes: only to these men do nothing; for therefore came they under the shadow of my roof.
9 Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
And they said, Stand back. And they said again, This one fellow came in to sojourn, and he will needs be a judge: now will we deal worse with you, than with them. And they pressed sore on the man, even Lot, and came near to break the door.
10 Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
But the men put forth their hand, and pulled Lot into the house to them, and shut to the door.
11 Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
And they smote the men that were at the door of the house with blindness, both small and great: so that they wearied themselves to find the door.
12 Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
And the men said to Lot, Have you here any besides? son in law, and your sons, and your daughters, and whatever you have in the city, bring them out of this place:
13 gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
For we will destroy this place, because the cry of them is waxen great before the face of the LORD; and the LORD has sent us to destroy it.
14 Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
And Lot went out, and spoke to his sons in law, which married his daughters, and said, Up, get you out of this place; for the LORD will destroy this city. But he seemed as one that mocked to his sons in law.
15 Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
And when the morning arose, then the angels hastened Lot, saying, Arise, take your wife, and your two daughters, which are here; lest you be consumed in the iniquity of the city.
16 Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
And while he lingered, the men laid hold on his hand, and on the hand of his wife, and on the hand of his two daughters; the LORD being merciful to him: and they brought him forth, and set him without the city.
17 Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
And it came to pass, when they had brought them forth abroad, that he said, Escape for your life; look not behind you, neither stay you in all the plain; escape to the mountain, lest you be consumed.
18 Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
And Lot said to them, Oh, not so, my LORD:
19 Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
Behold now, your servant has found grace in your sight, and you have magnified your mercy, which you have showed to me in saving my life; and I cannot escape to the mountain, lest some evil take me, and I die:
20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
Behold now, this city is near to flee to, and it is a little one: Oh, let me escape thither, (is it not a little one?) and my soul shall live.
21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
And he said to him, See, I have accepted you concerning this thing also, that I will not overthrow this city, for the which you have spoken.
22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
Haste you, escape thither; for I cannot do anything till you be come thither. Therefore the name of the city was called Zoar.
23 A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
The sun was risen on the earth when Lot entered into Zoar.
24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
Then the LORD rained on Sodom and on Gomorrah brimstone and fire from the LORD out of heaven;
25 Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
And he overthrew those cities, and all the plain, and all the inhabitants of the cities, and that which grew on the ground.
26 Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
But his wife looked back from behind him, and she became a pillar of salt.
27 Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
And Abraham got up early in the morning to the place where he stood before the LORD:
28 Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
And he looked toward Sodom and Gomorrah, and toward all the land of the plain, and beheld, and, see, the smoke of the country went up as the smoke of a furnace.
29 Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
And it came to pass, when God destroyed the cities of the plain, that God remembered Abraham, and sent Lot out of the middle of the overthrow, when he overthrew the cities in the which Lot dwelled.
30 Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
And Lot went up out of Zoar, and dwelled in the mountain, and his two daughters with him; for he feared to dwell in Zoar: and he dwelled in a cave, he and his two daughters.
31 Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
And the firstborn said to the younger, Our father is old, and there is not a man in the earth to come in to us after the manner of all the earth:
32 Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
Come, let us make our father drink wine, and we will lie with him, that we may preserve seed of our father.
33 A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
And they made their father drink wine that night: and the firstborn went in, and lay with her father; and he perceived not when she lay down, nor when she arose.
34 Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
And it came to pass on the morrow, that the firstborn said to the younger, Behold, I lay last night with my father: let us make him drink wine this night also; and go you in, and lie with him, that we may preserve seed of our father.
35 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
And they made their father drink wine that night also: and the younger arose, and lay with him; and he perceived not when she lay down, nor when she arose.
36 Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
Thus were both the daughters of Lot with child by their father.
37 ’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
And the first born bore a son, and called his name Moab: the same is the father of the Moabites to this day.
38 ’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.
And the younger, she also bore a son, and called his name Benammi: the same is the father of the children of Ammon to this day.

< Farawa 19 >