< Farawa 18 >

1 Ubangiji ya bayyana ga Ibrahim kusa da manyan itatuwan Mamre yayinda yake zaune a mashigin tentinsa da tsakar rana.
And YHWH appears to him among the oaks of Mamre, and he is sitting at the opening of the tent, about the heat of the day;
2 Da Ibrahim ya ɗaga ido, sai ya ga mutum uku suna tsaye kusa da shi. Sa’ad da ya gan su, sai ya tashi nan da nan daga mashigin tentinsa, ya tarye su, ya rusuna har ƙasa.
and he lifts up his eyes and looks, and behold, three men standing by him, and he sees, and runs to meet them from the opening of the tent, and bows himself toward the earth,
3 Ya ce, “Ranka yă daɗe, in na sami tagomashi daga gare ku kada ku wuce bawanku.
and he says, “My Lord, if now I have found grace in Your eyes, please do not pass on from Your servant;
4 Bari a kawo ruwa ku wanke ƙafafunku, ku huta a ƙarƙashin wannan itace.
please let a little water be accepted, and wash Your feet, and recline under the tree;
5 Bari in samo muku wani abu ku ci don ku wartsake, sa’an nan ku ci gaba da tafiyarku; da yake kun biyo wurin bawanku.” Suka ce, “To, sai ka yi abin da ka ce.”
and I bring a piece of bread, and support Your heart; afterward pass on, for therefore You have passed over to Your servant”; and they say, “So may you do as you have spoken.”
6 Saboda haka Ibrahim ya ruga zuwa wurin Saratu a cikin tenti ya ce, “Yi sauri, ki shirya mudu uku na gari mai laushi, ki cuɗa shi, ki yi burodi.”
And Abraham hurries toward the tent, to Sarah, and says, “Hurry three measures of flour-meal, knead, and make cakes”;
7 Sa’an nan Ibrahim ya yi gudu zuwa garkensa, ya zaɓi ɗan maraƙi ya ba wa bawansa, bawansa kuma ya yi sauri ya gyara shi.
and Abraham ran to the herd, and takes a son of the herd, tender and good, and gives to the young man, and he hurries to prepare it;
8 Sa’an nan Ibrahim ya ɗauko dambu da madara da naman ɗan maraƙin da aka gyara, ya kawo a gabansu. Yayinda suke ci, ya tsaya a gindin itace kusa da su.
and he takes butter and milk, and the son of the herd which he has prepared, and sets before them; and he is standing by them under the tree, and they eat.
9 Sai suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ibrahim ya ce, “Tana can cikin tenti.”
And they say to him, “Where [is] Sarah your wife?” And he says, “Behold—in the tent”;
10 Sa’an nan ɗayansu ya ce, “Lalle zan komo wurinka war haka shekara mai zuwa. Saratu matarka kuwa za tă haifi ɗa.” Saratu kuwa tana a bayansu tana ji daga mashigin tenti.
and He says, “Returning I return to you, about the time of life, and behold, to Sarah your wife a son.” And Sarah is listening at the opening of the tent, which is behind him;
11 Ibrahim da Saratu dai sun riga sun tsufa sosai. Saratu kuma ta wuce shekarun haihuwa.
and Abraham and Sarah [are] aged, entering into days—the way of women has ceased to be to Sarah;
12 Saboda haka Saratu ta yi dariya da ta yi tunani a zuci tana cewa, “Bayan ƙarfina ya ƙare, maigidana kuma ya tsufa, yanzu zan sami wannan jin daɗi?”
and Sarah laughs in her heart, saying, “After I have waxed old have I had pleasure? My lord [is] also old!”
13 Sai Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya har da ta ce, ‘Har zan iya haifi ɗa duk ta tsufata yanzu?’
And YHWH says to Abraham, “Why [is] this? Sarah has laughed, saying, Is it really true—I bear—and I am aged?
14 Akwai abin zai gagari Ubangiji? Zan komo wurinka a ƙayyadadden lokacin nan shekara mai zuwa kuma Saratu za tă haifi ɗa.”
Is anything too wonderful for YHWH? At the appointed time I return to you, about the time of life, and Sarah has a son.”
15 Saratu ta ji tsoro, don haka sai ta yi ƙarya ta ce, “Ban yi dariya ba.” Ya ce, “A’a, kin yi dariya.”
And Sarah denies, saying, “I did not laugh”; for she has been afraid; and He says, “No, but you did laugh.”
16 Sai mutanen suka tashi suka nufi Sodom, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya, ya yi bankwana da su.
And the men rise from there, and look on the face of Sodom, and Abraham is going with them to send them away;
17 Sai Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin yi?
and YHWH said, “Am I concealing from Abraham that which I am doing,
18 Lalle Ibrahim zai zama al’umma mai girma da kuma mai iko, kuma ta wurinsa dukan al’umman duniya za su sami albarka.
and Abraham certainly becomes a great and mighty nation, and blessed in him have been all nations of the earth?
19 Saboda na zaɓe shi don yă umarci’ya’yansa da iyalinsa a bayansa su kiyaye hanyoyin Ubangiji, ta wurin yin abin da yake daidai da kuma yin adalci, domin Ubangiji ya aikata abin da ya yi wa Ibrahim alkawari.”
For I have known him, that he commands his children, and his house after him (and they have kept the way of YHWH), to do righteousness and judgment, that YHWH may bring on Abraham that which He has spoken concerning him.”
20 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Kuka a kan Sodom da Gomorra ta yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni sosai,
And YHWH says, “The cry of Sodom and Gomorrah—because great; and their sin—because exceedingly grievous:
21 zan gangara in ga ko abin da suka yi ya yi muni kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.”
I go down now, and see whether according to its cry which is coming to Me they have done completely—and if not—I know”;
22 Sai mutanen suka juya suka nufi wajen Sodom amma Ibrahim ya ci gaba da kasance a gaban Ubangiji.
and the men turn from there, and go toward Sodom; and Abraham is yet standing before YHWH.
23 Sai Ibrahim ya matso wurinsa ya ce, “Za ka hallaka masu adalci tare da masu mugunta?
And Abraham draws near and says, “Do You also consume righteous with wicked?
24 Me zai faru in akwai mutum hamshin masu adalci a cikin birnin? Ashe, za ka hallaka shi, ba za ka cece wurin saboda mutane hamsin nan masu adalcin da suke a cikinsa ba?
Perhaps there are fifty righteous in the midst of the city; do You also consume, and not bear with the place for the sake of the fifty righteous who [are] in its midst?
25 Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba, ka kashe masu adalci tare da masu mugunta, ka ɗauka masu adalci da masu mugunta daidai? Tabbatacce ba za ka taɓa aikata irin wannan abu ba! Mai hukuncin dukan duniya ba zai aikata gaskiya ba?”
Far be it from You to do according to this thing, to put to death the righteous with the wicked; that it has been—as the righteous so the wicked—far be it from You; does the Judge of all the earth not do justice?”
26 Ubangiji ce, “In na sami mutum hamshin masu adalci a cikin birnin Sodom, zan bar dukan birnin saboda su.”
And YHWH says, “If I find in Sodom fifty righteous in the midst of the city, then have I borne with all the place for their sake.”
27 Sai Ibrahim ya ƙara cewa, “Yanzu da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, ko da yake ni ba kome ba ne illa turɓaya da toka,
And Abraham answers and says, “Now behold, I have willed to speak to the Lord, and I [am] dust and ashes;
28 in yawan masu adalci sun kāsa hamshin da mutum biyar fa? Za ka hallaka dukan birnin saboda rashin mutum biyar ɗin?” Ya ce, “In na sami mutum arba’in da biyar a wurin, ba zan hallaka shi ba.”
perhaps there are lacking five of the fifty righteous—do You destroy for five the whole of the city?” And He says, “I do not destroy [it], if I find there forty-five.”
29 Ya sāke cewa, “In mutum arba’in kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda mutum arba’in ɗin, ba zan aikata ba.”
And he adds again to speak to Him and says, “Perhaps there are found there forty?” And He says, “I do not do [it], because of the forty.”
30 Sai ya ce, “Kada Ubangiji ya yi fushi, amma bari in ƙara magana. A ce mutum talatin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Ba zan aikata ba, in na sami mutum talatin a can.”
And he says, “Please let it not be displeasing to the Lord, and I speak: perhaps there are found there thirty?” And He says, “I do not do [it], if I find there thirty.”
31 Ibrahim ya ce, “Yanzu fa da na yi karambani har na yi magana da Ubangiji, in ashirin kaɗai aka samu a can fa?” Ya ce, “Saboda ashirin ɗin, ba zan hallaka shi ba.”
And he says, “Now behold, I have willed to speak to the Lord: perhaps there are found there twenty?” And He says, “I do not destroy [it], because of the twenty.”
32 Sa’an nan Ibrahim ya ce, “Kada Ubangiji yă yi fushi, amma bari in ƙara magana sau ɗaya tak. In aka sami mutum goma kaɗai a can fa?” Ubangiji ya ce, “Saboda goma nan, ba zan hallaka shi ba.”
And he says, “Please let it not be displeasing to the Lord, and I speak only this time: perhaps there are found there ten?” And He says, “I do not destroy [it], because of the ten.”
33 Sa’ad da Ubangiji ya gama magana da Ibrahim, ya tafi, Ibrahim kuma ya koma gida.
And YHWH goes on, when He has finished speaking to Abraham, and Abraham has turned back to his place.

< Farawa 18 >