< Galatiyawa 6 >
1 ’Yan’uwa, in an kama wani yana cikin yin zunubi, ku da kuke masu ruhaniya ya kamata ku komo da shi a kan hanya a hankali. Amma ku lura da kanku, domin kada maimakon dawowa da ɗan’uwanku, ku ma ku fāɗi cikin jarraba.
Nobakwesu, naumwi wenu wajanika ulimukubisya, inywe nimuli amuuya mwelede kumuboozya amuuya muboombe. Amulikatazye lwenu nubeeni, ikuti inywebo mutasunkwi.
2 Ku ɗauki nawayar juna, a haka kuwa za ku cika dokar Kiristi.
Mubwezelane mukuli, mpawo muzuzikizye mulawu waKkilisito.
3 In wani yana tsammani shi wani abu ne alhali kuwa shi ba kome ba, ruɗin kansa yake yi.
Na umwi uyeeya kuti ulimbwabede wekatakwe mbwabede pe, ulikuyeeya lwakwe mwini.
4 Kowa yă auna ayyukansa. A sa’an nan ne zai iya yin taƙama da kansa, ba tare da kwatanta kansa da wani ba,
Awumwi alingule mulimo wakwe, mpawo kulikankayizya kwakwe kunoli mulinguwe kakutali kulumwi pe.
5 gama kowa zai ɗauki kayansa.
Kambo umwi awumwi uyonyampula mukuli wakwe.
6 Duk haka, wanda aka koya wa maganar Kiristi, bari yă raba abubuwan nan na alheri tare da wanda ya koyar da shi.
Ooyo uyiisigwa ijwi welede kwabilaana zintu zibotu awoyo uyiisya.
7 Kada a ruɗe ku. Ba a yi wa Allah ba’a. Mutum yakan girbe abin da ya shuka ne.
Muteeenwi pe. Leza tasekwi, kufumbwa muntu nchabyala, nchenchiicho nchayotebula.
8 Wanda ya yi shuki don yă gamshi mutuntakarsa, daga wannan mutuntaka zai girbi hallaka. Wanda ya yi shuki domin yă gamshi Ruhu, daga Ruhu zai girbi rai madawwami. (aiōnios )
Nkambo oyo ubyala imbuto munyama yakwe, kuzwa kunyama uyotebula lunyonyko. Kuli ooyo ubyala imbuto kumuuya kuzwa kumuuya uyotebula buumi ibutamani. (aiōnios )
9 Kada mu gaji da yin nagarta, gama a daidai lokaci za mu girbe amfani, in ba mu fid da zuciya ba.
Tutakatali mukuchita kabotu, nkambo kuchindi cheelede tuyotebula, kuti tetwakalengwana.
10 Saboda haka, in da hali, bari mu aikata nagarta ga dukan mutane, musamman ga waɗanda suke na iyalin masu bi.
Alimwi, nituchili amweenya, ngatuchitile bantu boonse bubotu, kwindilila abo bang'anda yalusyomo.
11 Ku dubi irin manya-manyan harufan da na yi amfani da su yayinda nake rubuta muku da hannuna!
Mulange kukomena kwamagwalo ngimulembela amaboko aangu.
12 Waɗanda suke son nuna bajinta a fili suna ƙoƙari su tilasta muku ku yi kaciya ne. Dalilin kaɗai da suke yin haka shi ne don gudu kada a tsananta musu saboda gicciyen Kiristi ne.
Abo bayanda kubotesya izyanyama balikweezya kumwangila ikuti mupalulwe. Balikuchita obo biyo kuti batapenzegwi nkambo kachiingano chaKkilisito.
13 Kai, su masu kaciya ma ba su kiyaye Doka ba, duk da haka suna so a yi muku kaciya don su yi taƙama kan an yi muku kaciya.
Nikuba kulaabo bakalipalula takwe nibakabamba mulawu, Pesi bayanda kuti mupalulwe ikuti bakali kankayizye nkambo kamibili yanu.
14 Kada in taɓa yin taƙama ga kome sai dai a cikin gicciyen Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa aka gicciye duniya a gare ni, aka kuma gicciye ni ga duniya.
Pesi nsyelede kulikankayizya pe kunze kwakulikankayizizya chiingano cha Mwami wesu Jesu Kkilisito, mukwiinda mulinchicho inyika yakakankaminwa alindime, andime kunyika.
15 Kaciya ko rashin kaciya ba wani abu ba ne; abin da yake da amfani shi ne sabuwar halitta.
Nikuba kupalulwa na kutapalulwa takwambi chintu pe, pesi chibaligwa biyo mbulenge bupya.
16 Salama da jinƙai su tabbata ga dukan waɗanda suke bin wannan ƙa’ida, har ma ga Isra’ila na Allah.
Kuli boonse benda munzila eeyi, lumuuno aluzyalo alube alimbabo nikuba kulabo bana ba Izilayili wa Leza.
17 A ƙarshe, kada kowa yă ƙara damuna, gama ina ɗauke da raunuka masu nuna ni bawan Ubangiji Yesu ne.
Kuzwa lino kutabi uchindikazya pe, nkambo amubili wangu ndibwezede impa zya Jesu.
18 ’Yan’uwa! Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ruhunku. Amin.
Luzyalo lwaMwami Jesu Kkilisito alube amyuuya yanu, nobakwesu, Amen.