< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
Då Esra så bad, bekände och gret, och låg inför Guds hus, församlade sig till honom utaf Israel en ganska stor menighet af män, qvinnor och barn; förty folket gret svårliga.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
Och Sechania, Jehiels son, af Elams barn, svarade, och sade till Esra: Si, vi hafve förtagit oss emot vår Gud, att vi hafve tagit oss främmande hustrur utaf landsens folk; men här är ännu hopp derom i Israel.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
Så låt oss nu göra ett förbund med vårom Gud, så att vi utdrifve alla hustrur, och dem som af dem födde äro, efter Herrans råd, och deras som frukta vår Guds bud, att man må göra efter lagen.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
Så statt nu upp; ty det hörer dig till: Vi vilje vara med dig; var vid en god tröst, och gör så.
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
Då stod Esra upp, och tog en ed af de öfversta Presterna, och Leviterna, och hela Israel, att de skulle göra efter detta talet. Och de svoro det.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
Och Esra stod upp inför Guds hus, och gick in uti Johanans, Eljasibs sons, kammar. Och då han ditkom, åt han intet bröd, och drack intet vatten; förty han sörjde öfver deras öfverträdelse, som i fängelset varit hade.
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
Och de läto utropa i Juda och Jerusalem, till all fängelsens barn, att de skulle församla sig till Jerusalem.
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
Och hvilken som icke komme innan tre dagar, efter öfverstarnas och de äldstas råd, hans ägodelar skulle alla tillspillogifvas, och han afskiljas ifrå fångarnas menighet.
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
Då församlade sig alle Juda män och BenJamin till Jerusalem, innan tre dagar; det är, på tjugonde dagen i den nionde månadenom. Och allt folket satt uppå gatone inför Guds hus, och bäfvade för detta ärendes skull, och för regnet.
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
Och Esra Presten stod upp, och sade till dem: I hafven förtagit eder, i det att I hafven tagit främmande hustrur, på det I skullen ännu föröka Israels skuld.
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
Så bekänner nu Herran edra fäders Gud, och görer det honom ljuft är, och skiljer eder ifrå landsens folk, och ifrå de främmande hustrur.
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
Då svarade hela menigheten, och sade med höga röst: Ske såsom du oss sagt hafver.
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
Men folket är mycket, och regnväder, och kan icke stå ute; så är det icke heller ens eller två dagars gerning; ty vi hafve sådana öfverträdelse mycken gjort.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
Låt oss beställa våra öfverstar i hela menighetene, att alle de i våra städer, som främmande hustrur tagit hafva, komma på bestämd tid; och de äldste i hvar staden, och deras domare med, tilldess vår Guds vrede må ifrån oss vänd varda i denna sakene.
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
Då vordo beställde Jonathan, Asahels son, och Jahesia, Thikva son, öfver denna saken; och Mesullam, och Sabbethai Leviterna hulpo dem.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
Och fängelsens barn gjorde alltså. Och Presten Esra, och de ypperste fäderne i deras fäders hus, och alle de nu nämnde äro, afskiljde sig, och satte sig på första dagen i tionde månadenom till att ransaka om detta ärendet.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
Och de uträttade det på alla de män, som främmande hustrur hade, på första dagen i första månadenom.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
Och vordo funne ibland Presternas barn, som främmande hustrur tagit hade, nämliga ibland Jesua barn, Jozadaks sons, och hans bröder: Maaseja, Elieser, Jarib och Gedalia.
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
Och de gåfvo deras hand deruppå, att de ville utdrifva hustrurna; och till deras skuldoffer offra en vädur för sina skuld.
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
Ibland Immers barn: Hanani och Sebadia.
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
Ibland Harims barn: Maaseja, Elia, Semaja, Jehiel och Ussia.
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
Ibland Pashurs barn: Eljoenai, Maaseja, Ismael, Nethaneel, Josabad och Eleasa.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
Ibland Leviterna: Josabad, Simei och Kelaja, den är Kelita; Pethabja, Juda och Elieser.
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
Ibland sångarena: Eljasib. Ibland dörravaktarena: Sallum, Telem och Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
Utaf Israel: Ibland Paros barn: Ramia, Jissija, Malchija, Mijamin, Eleazar, Malchija och Benaja.
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
Ibland Elams barn: Mattania, Zacharia, Jehiel, Abdi, Jeremoth och Elia.
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
Ibland Sattu barn: Eljoenai, Eljasib, Mattania, Jeremoth, Sabad och Asisa.
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
Ibland Bebai barn: Johanan, Hanania, Sabbai och Athlai.
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
Ibland Bani barn: Mesullam, Malluch, Adaja, Jasub, Seal och Jeramoth.
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
Ibland PahathMoabs barn: Adna, Chelal, Benaja, Maaseja, Mattania, Bezaleel, Binnui och Manasse.
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
Ibland Harims barn: Elieser, Jissija, Malchija, Semaja, Simeon,
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
BenJamin, Malluch och Semaria.
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
Ibland Hasums barn: Mattenai, Mattatta, Sabad, Elipheleth, Jeremai, Manasse och Simi.
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
Ibland Bani barn: Maadai, Amram, Uel,
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
Benaja, Bedja, Cheluhu,
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
Banja, Meremoth, Eljasib,
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
Mattania, Mattenai, Jaasav,
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
Bani, Binnui, Simi,
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
Selemia, Nathan, Adaja,
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
Machnadbai, Sasai, Sarai,
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
Asareel, Selemia, Semaria,
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
Sallum, Amaria och Joseph.
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
Ibland Nebo barn: Jegiel, Mattithia, Sabad, Sebina, Jaddai, Joel och Benaja.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
Desse hade alle tagit främmande hustrur; och voro somlige ibland de samma hustrur, som barn födt hade.

< Ezra 10 >