< Ezekiyel 44 >

1 Sai mutumin ya komo da ni zuwa ƙofar waje na wuri mai tsarki, wadda take fuskantar gabas, tana kuwa a rufe.
Puis il me fit revenir dans la direction du portique extérieur du sanctuaire qui regardait l’orient; il était fermé.
2 Ubangiji ya ce mini, “Wannan ƙofar za tă kasance a rufe. Ba za a buɗe ta ba; ba wanda zai shiga ta wurinta. Za tă kasance a rufe domin Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya shiga ta wurinta.
Et Yahweh me dit: « Ce portique sera fermé; il ne s’ouvrira point, et personne n’entrera par là, car Yahweh, le Dieu d’Israël, est entré par là; et il sera fermé.
3 Sarki kansa ne kaɗai zai zauna a hanyar shiga don yă ci a gaban Ubangiji. Zai shiga ta hanyar shirayin hanyar shiga yă kuma fita a wannan hanya.”
Quant au prince, comme étant le prince, il s’y assoira pour manger les mets devant Yahweh; il entrera par le chemin du vestibule du portique et sortira par le même chemin. »
4 Sa’an nan mutumin ya kawo ni ta hanyar ƙofar arewa zuwa gaban haikali. Na duba na kuma ga ɗaukakar Ubangiji tana cika haikalin Ubangiji, sai na fāɗi rubda ciki.
Il me conduisit ensuite dans la direction du portique septentrional, devant la maison; et je vis, et voici que la gloire de Yahweh remplissait la maison; et je tombai sur ma face.
5 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, ka lura sosai, ka saurara sosai ka kuma mai da hankali ga kome da na faɗa maka game da dukan ƙa’idodi game da haikalin Ubangiji. Ka lura sosai da ƙofar shigar haikali da kuma dukan ƙofofin wuri mai tsarki.
Et Yahweh me dit: « Fils de l’homme, applique ton cœur, regarde de tes yeux et écoute de tes oreilles tout ce que je vais te dire au sujet de toutes les ordonnances de la maison de Yahweh et de toutes ses lois. Applique ton cœur à ce qui doit entrer dans la maison, par toutes les issues du sanctuaire.
6 Faɗa wa’yan tawayen gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ayyukan banƙyamarku sun isa haka, ya gidan Isra’ila!
Dis aux rebelles, à la maison d’Israël: Ainsi parle le Seigneur Yahweh: C’est assez de toutes vos abominations, maison d’Israël,
7 Ban da dukan sauran ayyukanku na banƙyama, kun kawo baƙi marasa kaciya a zuciya da jiki a wurina mai tsarki, kun kuma ƙazantar da haikalina yayinda kuke miƙa mini abinci, kitse da kuma jini, kun kuma karya alkawarina.
assez d’avoir introduit des fils d’étranger, incirconcis de cœur et incirconcis de chair, pour qu’ils fussent dans mon sanctuaire, afin de profaner ma maison, quand vous offriez les mets qui m’appartiennent, la graisse et le sang; et ainsi ils ont rompu mon alliance par toutes vos abominations.
8 A maimakon yin ayyukanku bisa ga abubuwana masu tsarki, kun sa waɗansu su lura da wurina mai tsarki.
Vous ne vous êtes pas acquittés du service de mes choses saintes, et vous avez établi ces étrangers pour faire mon service, dans mon sanctuaire, à votre profit.
9 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba baƙo marar kaciya a zuciya da jiki da zai shiga wurina mai tsarki, kai, har ma da baƙin da suke zama a cikin Isra’ila.
Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Aucun fils d’étranger, incirconcis de cœur et incirconcis de chair, n’entrera dans mon sanctuaire; non, aucun des fils d’étranger qui sont au milieu des enfants d’Israël.
10 “‘Lawiyawan da suka yi nesa da ni sa’ad da Isra’ila suka kauce da kuma waɗanda suka karkata daga gare ni suka bi gumakansu, dole su ɗauki alhakin zunubinsu.
Bien plus, les Lévites qui se sont éloignés de moi au temps de l’égarement d’Israël, qui s’est égaré loin de moi pour suivre ses idoles infâmes, porteront leur iniquité.
11 Za su iya yin hidima a wurina mai tsarki, suna lura da ƙofofin haikali suna kuma hidima a cikinsu; za su iya yankan hadayun ƙonawa da sadaka don mutane su kuma tsaya a gaban mutane su yi musu hidima.
Ils seront dans mon sanctuaire des serviteurs préposés aux portes de la maison et faisant le service de la maison; ce sont eux qui égorgeront pour le peuple les victimes destinées à l’holocauste et aux autres sacrifices, et ils se tiendront devant le peuple pour le servir.
12 Amma domin sun yi musu hidima a gaban gumakansu suka sa gidan Isra’ila ya yi zunubi, saboda haka na ɗaga hannu na rantse cewa dole su ɗauki alhakin zunubinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Parce qu’ils l’ont servi devant ses idoles infâmes et qu’ils ont fait tomber la maison d’Israël dans l’iniquité, à cause de cela j’ai levé ma main sur eux, — oracle du Seigneur Yahweh, — jurant qu’ils porteraient leur iniquité.
13 Ba za su yi kusa don su yi hidima kamar firistoci ko su zo kusa da abubuwana masu tsarki ko hadayuna mafi tsarki ba; dole su sha kunya saboda ayyukansu na banƙyama.
Ils n’approcheront pas de moi pour remplir devant moi les fonctions du sacerdoce, pour s’approcher de toutes mes choses saintes, dans les lieux très saints; ils porteront leur opprobre et la peine des abominations qu’ils ont commises.
14 Duk da haka zan sa su su lura da ayyukan haikali da kuma dukan ayyukan da za a yi a cikinsa.
Je les chargerai de faire le service de la maison, pour tout son ouvrage, et pour tout ce qui s’y doit faire.
15 “‘Amma firistoci, waɗanda suke Lawiyawa kuma zuriyar Zadok waɗanda suka yi aminci ta wurin yin ayyukansu a wurina mai tsarki sa’ad da Isra’ilawa suka kauce daga gare ni, su ne za su zo kusa don hidima a gabana; za su tsaya a gabana don miƙa hadayun kitse da jini, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Mais les prêtres lévites, fils de Sadoc, qui ont gardé les observances de mon sanctuaire quand les enfants d’Israël s’égaraient loin de moi, ce sont eux qui s’approcheront de moi pour faire mon service et qui se tiendront devant moi pour m’offrir la graisse et le sang, — oracle du Seigneur Yahweh.
16 Su ne kaɗai za su shiga wurina mai tsarki; su ne kaɗai za su zo kusa da teburina don yin hidima a gabana su kuma yi hidimata.
Ce sont eux qui entreront dans mon sanctuaire, eux qui s’approcheront de ma table pour faire mon service, et ils garderont mes observances.
17 “‘Sa’ad da suka shiga ƙofofin fili na can ciki, dole su sa tufafin lilin; kada su sa wani rigar da aka yi da ulu yayinda suke hidima a ƙofofin fili na can ciki da cikin haikali.
Lorsqu’ils franchiront les portiques du parvis intérieur, ils se vêtiront d’habits de lin; il n’y aura pas de laine sur eux, quand ils feront le service dans les portiques du parvis intérieur et au-dedans.
18 Za su naɗa rawunan lilin a kawunansu, su kuma sa wandunan lilin. Kada su sa wani abin da zai sa su yi zuffa.
Ils auront des mitres de lin sur la tête; et ils auront des caleçons de lin sur les reins; et ils ne se ceindront pas de ce qui exciterait la sueur.
19 Sa’ad da suka fita daga haikali zuwa fili na waje inda mutane suke, sai su tuɓe rigunan da suka yi hidima da su su bar su a tsarkakan ɗakuna, su sa waɗansu riguna, don kada su tsarkake mutane ta wurin rigunansu.
Mais lorsqu’ils sortiront au parvis extérieur, au parvis extérieur vers le peuple, ils ôteront leurs vêtements avec lesquels ils ont fait le service, ils les déposeront dans les chambres du sanctuaire; et ils revêtiront d’autres vêtements et ne sanctifieront pas le peuple par leurs vêtements.
20 “‘Ba za su aske kawunansu ko su bar gashin kansu ya yi tsayi ba, amma sai su sausaye gashin kansu.
Ils ne se raseront pas la tête et ne laisseront pas non plus croître leurs cheveux; ils se tondront la tête.
21 Kada firist ya sha ruwan inabi sa’ad da zai shiga fili na can ciki.
Aucun prêtre ne boira du vin lorsqu’il entrera dans le parvis intérieur.
22 Kada su auri gwauruwa ko macen da aka sāke; za su auri budurwai ne kaɗai na Isra’ilawa ko gwaurayen firistoci.
Ils ne prendront pour femme ni une veuve ni une femme répudiée, mais seulement des vierges de la race de la maison d’Israël; ils pourront prendre une veuve qui sera la veuve d’un prêtre.
23 Za su koyar da mutanena bambanci tsakanin tsarki da rashin tsarki su kuma nuna musu yadda za su bambanta marar tsarki da mai tsarki.
Ils instruiront mon peuple à distinguer entre ce qui est saint et ce qui est profane; ils lui apprendront à distinguer entre ce qui est souillé et ce qui est pur.
24 “‘A duk wani rashin jituwa, firistoci za su zama alƙalai su kuma yanke magana bisa ga farillaina. Za su kiyaye dokokina da ƙa’idodina a dukan ƙayyadaddun bukukkuwana, su kuma kiyaye Asabbataina da tsarki.
Dans les contestations, ce sont eux qui prendront place pour le jugement, et ils jugeront d’après le droit que j’ai établi. Ils observeront mes lois et mes ordonnances dans toutes mes fêtes, et ils sanctifieront mes sabbats.
25 “‘Firist ba zai ƙazantar da kansa ta wurin zuwa kusa da gawa ba; amma, in gawar mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ko ɗansa ko’yarsa, ko ɗan’uwansa ko’yar’uwarsa ce, to, ba zai ƙazantar da kansa ba.
Aucun d’eux n’ira auprès du cadavre d’un homme pour se souiller; ils ne pourront se souiller que pour un père ou une mère, pour un fils ou une fille, pour un frère ou une sœur qui n’a pas de mari.
26 Bayan ya tsarkaka, dole yă jira har kwana bakwai.
Après sa purification, on lui comptera sept jours,
27 A ranar da ya shiga fili na can ciki na wuri mai tsarki don hidima a wuri mai tsarki, zai miƙa hadaya don zunubi saboda kansa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
et le jour où il entrera dans le lieu saint, au parvis intérieur, pour faire le service dans le sanctuaire, il offrira son sacrifice pour le péché, — oracle du Seigneur Yahweh.
28 “‘Ni ne kaɗai zan zama abin gādon da firistoci za su kasance da shi. Kada ka ba su wani mallaka a Isra’ila; zan zama mallakarsu.
Voici l’héritage qu’ils auront: Je serai leur héritage; vous ne leur donnerez pas de possession en Israël, c’est moi qui suis leur possession.
29 Za su ci hadaya ta gari, hadaya don zunubi da hadaya don laifi; da kuma kowane keɓaɓɓen abu a Isra’ila da za a ba wa Ubangiji zai zama nasu.
Ils se nourriront de l’oblation, du sacrifice pour le péché et du sacrifice pour le délit; et tout ce qui aura été dévoué par anathème en Israël sera pour eux.
30 Mafi kyau na nunan farinku da kuma dukan kyautanku na musamman za su zama na firistoci. Za ku ba su rabo na fari na ɓarzajjen hatsinku saboda albarka ta kasance a gidanku.
Les prémices de tous les premiers produits de toutes sortes et toutes les offrandes de toutes sortes de tout ce que vous offrirez seront pour les prêtres; vous donnerez aussi aux prêtres les prémices de vos moutures, afin que la bénédiction repose sur ta maison.
31 Firistoci ba za su ci mushen tsuntsu ko na dabba ba, ba kuwa za su ci waɗanda namun jeji suka kashe ba.
Tout animal mort ou déchiré, soit oiseau, soit autre bête, les prêtres ne le mangeront pas. »

< Ezekiyel 44 >