< Ezekiyel 43 >

1 Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
Puis, il me conduisit à la porte, à cette porte qui est disposée du côté de l’Est.
2 sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
Et voici que la gloire du Dieu d’Israël s’avançait du côté de l’Est; son grondement ressemblait au bruit de grandes eaux, et la terre s’illuminait de sa gloire.
3 Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
Cette vision était pareille à la vision qui m’était apparue, à la vision que j’avais eue en venant pour la destruction de la ville; c’étaient des visions comme celle que j’avais eue sur le fleuve de Khebar, et je tombai sur ma face.
4 Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
La gloire de l’Eternel entra dans le temple par la porte qui est tournée du côté de l’Est.
5 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Et l’esprit me souleva et m’amena dans le parvis intérieur, et voici que la gloire de l’Eternel remplissait le temple.
6 Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
J’Entendis quelqu’un me parler du fond du temple, tandis que l’homme se tenait debout auprès de moi.
7 Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
Il me dit: "Fils de l’homme, c’est ici l’emplacement de mon trône, le lieu où se pose la plante de mes pieds, où je résiderai à jamais au milieu des enfants d’Israël. Désormais la maison d’Israël ne profanera plus mon saint nomni eux, ni leurs roispar leurs prostitutions et les cadavres de leurs rois sur leurs hauts-lieux;
8 Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
car ils mettaient leur seuil près de mon seuil, leurs poteaux près de mes poteaux, avec un simple mur entre moi et eux. C’Est ainsi qu’ils profanaient mon nom par les abominations qu’ils commettaient, et que je les ai consumés dans ma colère.
9 Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
A présent, ils éloigneront de moi leurs prostitutions et les cadavres de leurs rois, et je résiderai parmi eux pour toujours.
10 “Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
Toi, fils de l’homme, décris le temple à la maison d’Israël, pour qu’ils rougissent de leurs iniquités; qu’ils en vérifient le plan!
11 kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
S’Ils rougissent de tout ce qu’ils ont fait, expose-leur et dessine devant eux le plan du temple, ses dispositions, ses issues, ses accès, toutes ses parties, ses dimensions, sa forme et son ordonnance; qu’ils en retiennent tout le plan et l’architecture, afin de les exécuter.
12 “Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
Voici la règle relative au temple: situé sur le sommet de la montagne, tout son circuit à l’entour est éminemment saint. Telle est la règle relative au temple.
13 “Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
Et voici les dimensions de l’autel en coudées, chaque coudée valant une coudée et une palme: la cavité est d’une coudée de profondeur, plus une coudée de largeur, le rebord qui le limite à l’entour ayant un empan pour chaque face; tel est le support de l’autel.
14 Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
Depuis la cavité du sol jusqu’à la saillie inférieure, deux coudées; largeur, une coudée. Depuis la petite saillie jusqu’à la grande saillie, quatre coudées, sur une de largeur.
15 Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
Pour le harêl, quatre coudées de hauteur, et au-dessus de l’ariêl s’élèvent les quatre cornes.
16 Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
L’Ariêl, long de douze coudées sur douze de large, forme un carré par ses quatre côtés.
17 Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
L’Enceinte a donc quatorze coudées de long sur quatorze de large, formant un carré par ses quatre côtés; le rebord qui le circonscrit a une demi-coudée, et la cavité intérieure une coudée en tous sens. Ses degrés sont dans la direction de l’Orient."
18 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
Il me dit: "Fils de l’homme, ainsi parle le Seigneur Dieu: Voici quelles seront les règles de l’autel, du jour où il aura été construit: on y offrira des holocaustes et l’on y aspergera du sang.
19 Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Tu donneras aux pontifesaux Lévites qui sont de la lignée de Çadokqui s’approchent de moi, dit le Seigneur Dieu, pour me servir, un jeune taureau comme expiatoire.
20 Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
Tu prendras de son sang, que tu appliqueras aux quatre cornes, aux quatre angles de la saillie et tout autour du rebord; par là tu le purifieras et tu lui ôteras sa souillure.
21 Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
Puis tu enlèveras ce taureau expiatoire, qu’on brûlera dans la dépendance du temple désignée pour cela, en dehors du sanctuaire.
22 “A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
Le deuxième jour, tu offriras comme expiatoire un bouc sans défaut, et l’on purifiera l’autel comme on l’aura purifié par le taureau.
23 Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
La purification terminée, tu présenteras un jeune taureau sans défaut et un bélier sans défaut choisi dans le menu bétail.
24 Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
Tu les présenteras devant l’Eternel; les pontifes y répandront du sel et les offriront en holocauste à l’Eternel.
25 “Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
Sept jours durant, tu offriras chaque jour un bouc expiatoire; puis on offrira un jeune taureau et un bélier du menu bétail, on les offrira sans défaut.
26 Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
On mettra sept jours à faire l’expiation de l’autel, à le purifier et à l’inaugurer.
27 A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Quand on aura épuisé cette série de jours, c’est-à-dire à partir du huitième jour, les pontifes offriront sur l’autel vos holocaustes et vos rémunératoires, et je vous serai propice, dit le Seigneur Dieu."

< Ezekiyel 43 >