< Ezekiyel 37 >

1 Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
RAB'bin eli üzerimdeydi, Ruhu'yla beni dışarı çıkardı, kemiklerle dolu bir ovanın ortasına koydu.
2 Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
Beni onların arasında her yöne dolaştırdı. Ovada her yere yayılmış, tamamen kurumuş pek çok kemik vardı.
3 Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
RAB, “İnsanoğlu, bu kemikler canlanabilir mi?” diye sordu. Ben, “Sen bilirsin, ey Egemen RAB” diye yanıtladım.
4 Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
Bunun üzerine, “Bu kemikler üzerine peygamberlik et” dedi, “Onlara de ki, ‘Kuru kemikler, RAB'bin sözünü dinleyin!
5 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
Egemen RAB bu kemiklere şöyle diyor: İçinize ruh koyacağım, canlanacaksınız.
6 Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Size kaslar verecek, üzerinizde et oluşturacağım, sizi deriyle kaplayacağım. İçinize ruh koyacağım, canlanacaksınız. O zaman benim RAB olduğumu anlayacaksınız.’”
7 Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
Böylece bana verilen buyruk uyarınca peygamberlik ettim. Ben peygamberlik ederken bir gürültü oldu, bir takırtı duyuldu. Kemikler birbirleriyle birleşiyordu.
8 Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
Baktım, işte üzerlerinde kaslar, etler oluşuyor, üstlerini deri kaplıyordu. Ama onlarda ruh yoktu.
9 Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
Sonra bana şöyle dedi: “Rüzgara peygamberlik et, insanoğlu, peygamberlik et ve de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Ey rüzgar, gel dört yandan es. Bu öldürülmüşlerin üzerine üfle ki canlansınlar!’”
10 Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
Böylece bana verilen buyruk uyarınca peygamberlik ettim. Onların içine soluk girince canlanıp ayağa kalktılar. Çok, çok büyük bir kalabalık oluşturuyorlardı.
11 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
Sonra bana, “İnsanoğlu, bu kemikler bütün İsrail halkını simgeliyor” dedi, “Onlar, ‘Kemiklerimiz kurudu, umudumuz yok oldu, bittik’ diyorlar.
12 Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
Bu yüzden peygamberlik et ve onlara de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: Ey halkım, mezarlarınızı açıp sizi oradan çıkaracak, İsrail ülkesine geri getireceğim.
13 Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
Mezarlarınızı açıp sizi çıkardığım zaman benim RAB olduğumu anlayacaksınız, ey halkım.
14 Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
Ruhumu içinize koyacağım, canlanacaksınız. Sizi kendi ülkenize yerleştireceğim. O zaman, bunu söyleyenin ve yapanın ben RAB olduğumu anlayacaksınız.’” Böyle diyor RAB.
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
RAB bana şöyle seslendi:
16 “Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
“İnsanoğlu, bir değnek al, üzerine ‘Yahuda ve dostları İsrailliler için’ diye yaz. Sonra başka bir değnek al, üzerine ‘Yusuf'la dostları İsrailliler için Efrayim'in değneği’ diye yaz.
17 Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
İki değneği yan yana getirerek birleştir. Öyle ki, elinde bir değnek gibi olsun.
18 “In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
“Halkından biri, ‘Bu yaptığının anlamı ne? Bize açıklamaz mısın?’ diye sorarsa,
19 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
şöyle yanıtlayacaksın: ‘Egemen RAB şöyle diyor: Efrayim'in elindeki değneği –Yusuf'la dostları İsrail oymaklarının değneğini– alıp Yahuda değneğiyle birleştireceğim. İkisinden bir değnek yapıp elimde tutacağım.’
20 Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
Üzerine yazdığın değnekleri görebilecekleri şekilde elinde tut.
21 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
Onlara de ki, ‘Egemen RAB şöyle diyor: İsrailliler'i gittikleri ulusların içinden alacağım. Onları her yerden toplayıp ülkelerine geri getireceğim.
22 Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
Onları ülkede, İsrail dağları üzerinde tek bir ulus yapacağım. Hepsinin tek kralı olacak. Artık iki ayrı ulus olmayacaklar, iki krallığa bölünmeyecekler.
23 Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
Artık putlarıyla, iğrenç uygulamalarıyla, isyanlarıyla kendilerini kirletmeyecekler. Onları yerleştikleri, içinde günah işledikleri yerlerden kurtarıp arındıracağım. Onlar halkım olacak, ben de onların Tanrısı olacağım.
24 “‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
“‘Kulum Davut onların kralı olacak, hepsinin tek çobanı olacak. Buyruklarımı izleyecek, kurallarıma uyacak, onları uygulayacaklar.
25 Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
Kulum Yakup'a verdiğim, atalarınızın yaşadığı ülkeye yerleşecekler. Kendileri, çocukları, çocuklarının çocukları sonsuza dek orada yaşayacaklar. Kulum Davut da sonsuza dek onların önderi olacak.
26 Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
Onlarla esenlik antlaşması yapacağım. Bu onlarla sonsuza dek geçerli bir antlaşma olacak. Onları yeniden oraya yerleştirip sayıca çoğaltacağım. Tapınağımı sonsuza dek onların ortasına kuracağım.
27 Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
Konutum aralarında olacak; onların Tanrısı olacağım, onlar da benim halkım olacak.
28 Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”
Tapınağım sonsuza dek onların arasında oldukça uluslar İsrail'i kutsal kılanın ben RAB olduğumu anlayacaklar.’”

< Ezekiyel 37 >