< Ezekiyel 37 >

1 Hannun Ubangiji yana a kaina, ya kuma fitar da ni ta wurin Ruhun Ubangiji ya sa ni a tsakiyar kwarin; yana cike da ƙasusuwa.
Et la main du Seigneur fut sur moi, et le Seigneur me ravit en esprit; et il me déposa au milieu d'un champ, et ce champ était rempli d'ossements humains.
2 Ya sa na kai na komo a ciki, na kuma ga ƙasusuwa masu girma da yawa a ƙasar kwarin, ƙasusuwan da suka bushe ƙwarai.
Et le Seigneur me conduisit tout autour de ces os, et voilà qu'il y en avait une multitude sur la surface du champ, et ils étaient tout desséchés.
3 Sai ya tambaye ni cewa, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa za su iya rayu?” Ni kuwa na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kai kaɗai ka sani.”
Et le Seigneur me dit: Fils de l'homme, ces os revivront-ils? Et je répondis: Seigneur, Seigneur, vous le savez.
4 Sai ya ce mini, “Ka yi wa waɗannan ƙasusuwa annabci ka ce musu, ‘Busassun ƙasusuwa, ku ji maganar Ubangiji!
Et il me dit: Prophétise sur ces ossements, et dis-leur: Ossements desséchés, écoutez la parole du Seigneur.
5 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa waɗannan ƙasusuwa. Zan sa numfashi ya shiga muku, za ku kuwa rayu.
Or voici ce que dit le Seigneur à ces ossements: Je vais amener sur vous un souffle de vie,
6 Zan harhaɗa muku jijiyoyi in sa muku tsoka in kuma rufe ku da fata; zan sa numfashi a cikinku, za ku kuwa rayu. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Et je poserai sur vous des nerfs, et j'amènerai sur vous des chairs, et sur vous j'étendrai de la peau, et je mettrai en vous mon souffle, et vous vivrez, et vous saurez que je suis le Seigneur.
7 Saboda haka sai na yi annabci yadda aka umarce ni. Da nake annabcin, sai aka ji motsi, ƙarar girgiza, sai ƙasusuwan suka harhaɗu, ƙashi ya haɗu da ƙashi.
Et je prophétisai comme le Seigneur me l'avait prescrit, et ceci advint pendant que je prophétisais: Voilà que les ossements s'agitèrent et vinrent se placer chacun dans sa jointure.
8 Na duba, sai ga jijiyoyi da nama suka bayyana a kansu fata kuma ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu.
Et je regardai; et voilà que sur les os des nerfs et des chairs se produisirent, et de la peau les recouvrit; mais l'esprit n'était pas encore en eux.
9 Sa’an nan ya ce mini, “Ka yi annabci wa numfashi; ka yi annabci, ɗan mutum, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ka fito daga kusurwoyi huɗu, ya numfashi, ka kuma numfasa cikin waɗannan matattu, don su rayu.’”
Et le Seigneur me dit: Prophétise à l'esprit, prophétise, fils de l'homme, et dis à l'esprit: Voici ce que dit le Seigneur: Viens des quatre vents, et souffle dans ces morts, et qu'ils vivent.
10 Saboda haka na yi annabci yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga musu; suka rayu suka kuma miƙe tsaye a ƙafafunsu babbar runduna ce ƙwarai.
Et je prophétisai comme le Seigneur me l'avait prescrit, et l'esprit entra dans les morts, et ils furent vivants, et ils se dressèrent sur leurs pieds en immense multitude.
11 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa su ne dukan gidan Isra’ila. Suna cewa, ‘Ƙasusuwanmu sun bushe, sa zuciyarmu duk ya tafi; an share mu ƙaf.’
Et le Seigneur me parla, disant: Fils de l'homme, ces os sont toute la maison d'Israël, et eux-mêmes disent: Nos ossements sont desséchés, notre espérance a péri, et nous sommes sans voix.
12 Saboda haka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ya mutanena, zan buɗe kaburburanku in fitar da ku daga cikinsu; zan mai da ku ƙasar Isra’ila.
À cause de cela, prophétise et dis: Voilà que j'ouvre vos sépulcres, dit le Seigneur; je vais vous en faire sortir, et je vous introduirai en la terre d'Israël;
13 Sa’an nan ku, mutanena, za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na buɗe kaburburanku na fitar da ku daga cikinsu.
Et vous saurez que moi je suis le Seigneur, quand j'aurai ouvert vos sépulcres, et que de ces sépulcres j'aurai tiré mon peuple.
14 Zan sa Ruhuna a cikinku za ku kuwa rayu, zan kuma zaunar da ku a ƙasarku. Sa’an nan za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata, in ji Ubangiji.’”
Et je vous donnerai mon esprit, et vous vivrez, et je vous établirai sur votre terre, et vous saurez que je suis le Seigneur. J'ai parlé, et j'exécuterai, dit le Seigneur.
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me vint, disant:
16 “Ɗan mutum, ka ɗauki sanda ka rubuta a kansa, ‘Na Yahuda da Isra’ilawan da suke tare da shi.’ Sa’an nan ka ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Sandan Efraim, na Yusuf da dukan gidan Isra’ilan da suke tare da shi.’
Fils de l'homme, prends une baguette, et sur elle écris: Juda et tous les enfants d'Israël de son parti. Prends une autre baguette, et écris sur elle: Pour Joseph; puis une baguette pour Ephraïm; inscris enfin tous les enfants appartenant à Israël.
17 Ka haɗa su su zama sanda guda saboda su kasance ɗaya a hannunka.
Et tu les réuniras ensemble pour n'être qu'une baguette, après les avoir liées, et elles seront dans ta main.
18 “In mutanen ƙasarka suka tambaye ka cewa, ‘Ba za ka faɗa mana abin da kake nufi da wannan ba?’
Et ceci adviendra: Lorsque les enfants de ton peuple te diront: Ne nous expliqueras-tu point ce que cela signifie?
19 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Zan ɗauki sandan Yusuf, wanda yake a hannun Efraim, da na kabilan Isra’ilawan da suke tare da shi, in haɗa shi da sandan Yahuda, in mai da su sanda guda, za su kuwa zama ɗaya a hannuna.’
Tu leur diras: Ainsi parle le Seigneur: Voilà que je vais prendre la tribu de Joseph, qui est dans la main d'Éphraïm, et les tribus d'Israël qui appartiennent à celle-ci, et je les réunirai à la tribu de Juda, et elles ne formeront qu'une baguette dans la maison de Juda.
20 Ka riƙe sandunan da ka yi rubutun a gabansu
Et les baguettes sur lesquelles tu as écrit seront en ta main en présence du peuple.
21 ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan fitar da Isra’ilawa daga al’ummai inda suka tafi. Zan tattara su daga dukan kewaye in komo da su ƙasarsu.
Et tu leur diras: Ainsi parle le Seigneur Maître: Voilà que je vais retirer toute la maison d'Israël du milieu des nations où elle est entrée; je les rassemblerai d'entre toutes les contrées d'alentour, et je les ramènerai en la terre d'Israël.
22 Zan mai da su al’umma ɗaya a cikin ƙasar, a kan duwatsun Isra’ila. Za a kasance da sarki guda a kan dukansu ba za su ƙara zama al’ummai biyu ko su rabu su zama masarautai biyu ba.
Et j'en ferai une nation dans la terre qui m'appartient et sur les montagnes d'Israël. Et il y aura pour eux un seul prince, et ils ne formeront plus deux nations, et ils ne seront plus jamais divisés en deux royaumes,
23 Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da mugayen siffofi ko kuma da wani daga laifofinsu ba, gama zan cece su daga dukan zunubinsu na ridda, zan kuma tsarkake su. Za su zama mutanena, ni kuma zan zama Allahnsu.
Afin de ne plus se souiller de leurs idoles; et je les préserverai de tous les dérèglements où ils sont tombés, et je les purifierai; et ils seront mon peuple, et moi, le Seigneur, je serai leur Dieu.
24 “‘Bawana Dawuda zai zama sarki a kansu, dukansu kuwa za su kasance da makiyayi guda. Za su bi dokokina su kuma kiyaye ƙa’idodina.
Et mon serviteur David sera prince au milieu d'eux; y aura pour eux tous un seul pasteur, parce qu'ils marcheront dans la voie de mes ordonnances et qu'ils garderont mes commandements et les pratiqueront.
25 Za su zauna a ƙasar da na ba wa bawana Yaƙub, ƙasar da kakanninsu suka zauna. Su da’ya’yansu da’ya’ya’ya’yansu za su zauna a can har abada, kuma Dawuda bawana zai zama sarkinsu har abada.
Et ils habiteront leur terre que j'ai donnée à mon serviteur Jacob, que leurs pères ont habitée; et eux-mêmes y habiteront. Et David, mon serviteur, sera leur prince dans tous les siècles.
26 Zan yi alkawarin salama da su; zai zama madawwamin alkawari. Zan kafa su in ƙara yawansu, zan kuma sa wuri mai tsarkina a cikinsu har abada.
Et je ferai avec eux une alliance de paix; et mon alliance avec eux sera éternelle. Et j'établirai au milieu d'eux mon sanctuaire dans tous les siècles.
27 Mazaunina zai kasance da su; zan kuwa zama Allahnsu, za su kuma zama mutanena.
Et mon tabernacle sera chez eux, et je serai leur Dieu; et ils seront mon peuple.
28 Sa’an nan al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji na mai da Isra’ila mai tsarki, sa’ad da wuri mai tsarkina yana a cikinsu har abada.’”
Et les nations sauront que je suis le Seigneur qui sanctifie les fils d'Israël, en établissant chez eux mon sanctuaire pour tous les siècles.

< Ezekiyel 37 >