< Ezekiyel 35 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A message from the Lord came to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir; ka yi annabci a kansa
“Son of man, face towards Mount Seir and prophesy against it
3 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, Dutsen Seyir, zan kuma miƙa hannuna gāba da kai in mai da kai kango.
Announce that this is what the Lord God says: Watch out, because I'm condemning you, Mount Seir. I'm going to attack you and turn you into a wasteland.
4 Zan mai da garuruwanka kufai za ka kuma zama kango. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
I will ruin your towns; you will be completely devastated. Then you will acknowledge that I am the Lord.
5 “‘Domin ka riƙe ƙiyayya ta tun dā, ka kuma ba da mutanen Isra’ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, lokacin da adadin horonsu ya cika,
Because of your lasting hatred for the Israelites you let them be attacked with swords as they went through terrible disasters when the time of their punishment was coming to an end.
6 saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sa a zub da jininka zan kuwa fafare ka. Da yake ba ka ƙi zub da jini ba, zub da jini zai fafare ka.
So as I live, declares the Lord God, I will let you be violently attacked and chased down. Since you did not hate bloodshed, bloodshed will come after you.
7 Zan mai da Dutsen Seyir kango in kuma yanke dukan waɗanda suke shiga da fita a cikinka.
I will turn Mount Seir into a ruined wasteland. I will wipe out anyone who leaves or who tries to return.
8 Zan cika duwatsunka da matattu; waɗanda aka kashe da takobi za su fāɗi a kan tuddanka, da cikin kwarurukanka, da cikin dukan kwazazzabanka.
I will fill its mountains with the dead. Those killed by the sword will fall in your hills, valleys, and all your ravines.
9 Zan mai da kai kango har abada; ba za a zauna a cikin garuruwanka ba. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.
I will ruin you forever. Your towns will not be inhabited again. Then you will acknowledge that I am the Lord.
10 “‘Domin kun ce, “Waɗannan al’ummai biyu da ƙasashe za su zama namu za mu kuma mallake su,” ko da yake Ni Ubangiji ina a can,
Because you said, ‘These two nations and their lands belong to us, and we will take them over, even though the Lord was there with them,’
11 saboda haka muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan sāka maka gwargwadon fushi da kuma kishin da ka nuna a ƙiyayyarsu da ka yi zan kuma sanar da kaina a cikinsu sa’ad da na hukunta ka.
then as I live, declares the Lord God, I will deal with you in the same way that you showed anger and jealousy to them in your hatred of them. They will realize that I'm punishing you because of the way you treated them.
12 Sa’an nan za ka san cewa Ni Ubangiji na ji duk abubuwan banzan da ka faɗa a kan duwatsun Isra’ila. Ka ce, “An mai da su kango an kuma ba mu su mu cinye.”
You will also realize that I, the Lord, heard all the nasty things you said about the mountainous land of Israel when you announced, ‘The mountains have been left empty; they're ours to take!’
13 Ka yi fariya a kaina, ka kuma yi magana a kaina ba gaggautawa, na ji shi sarai.
You made a lot of boasts attacking me—you had much to say against me. I heard it for myself!
14 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa yayinda dukan duniya take farin ciki, zan mai da kai kango.
This is what the Lord God says: I will destroy you as everyone else in the world celebrates.
15 Domin ka yi farin ciki sa’ad da gādon gidan Isra’ila ya zama kufai, haka zan yi da kai, ya Dutsen Seyir, kai da dukan Edom. Sa’an nan za ka san cewa ni ne Ubangiji.’”
Just as you celebrated when Israel was destroyed, I will do the same to you. Mount Seir, you will become a wasteland, and so will the rest of Edom. Then they will acknowledge that I am the Lord.”