< Ezekiyel 34 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Et la parole du Seigneur me vint, disant:
2 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
Fils de l'homme, prophétise contre les pasteurs d'Israël; prophétise, et dis aux pasteurs: Voici ce que dit le Seigneur Maître: Malheur aux pasteurs d'Israël! Est-ce que les pasteurs se paissent eux-mêmes? Est-ce que les pasteurs ne doivent pas paître les brebis?
3 Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
Voilà que vous mangez le laitage; vous vous faites des vêtements avec la laine; vous égorgez les bêtes les plus grasses; vous ne paissez point mes brebis.
4 Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
Vous n'avez point fortifié les faibles, vous n'avez point guéri les malades, vous n'avez point entouré de bandes les blessées, vous n'avez point ramené les égarées; vous n'avez point cherché ce qui était perdu; et ce qui était plein de force, vous l'avez accablé de labeurs.
5 Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
Aussi mes brebis ont été dispersées, parce qu'elles n'avaient pas de pasteurs; et elles ont été la pâture des bêtes fauves des champs.
6 Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
Et mes brebis ont été dispersées dans toutes les montagnes et sur toutes les hautes collines; elles ont été dispersées sur toute la face de la terre; et il n'y avait personne pour les chercher et les ramener.
7 “‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
À cause de cela, pasteurs, écoutez la parole du Seigneur:
8 Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
Par ma vie, dit le Seigneur Maître, en punition de ce que mes brebis ont été une proie, de ce que mes brebis ont été dévorées par toutes les bêtes fauves des champs, parce qu'elles n'avaient pas de pasteurs, et que les pasteurs ne cherchaient pas mes brebis, et que les pasteurs se paissaient eux-mêmes et ne paissaient pas mes brebis;
9 saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
En punition de cela, pasteurs,
10 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
Ainsi dit le Seigneur Maître: Voilà que je suis contre les pasteurs, et je réclamerai mes brebis de leurs mains, et je les empêcherai de paître mes brebis, et les pasteurs ne les feront plus paître; je retirerai mes brebis de leur bouche, et ils ne s'en nourriront plus.
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
Car ainsi dit le Seigneur Maître: Voilà que je vais moi-même chercher mes brebis, et je les visiterai.
12 Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
Tel le pâtre cherche ses troupeaux le jour où il y a des nuages et des ténèbres, au milieu des brebis dispersées, tel je chercherai mes brebis, et je les ramènerai de tous les lieux où elles auront été dispersées dans les jours de ténèbres et de nuages.
13 Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
Et je les retirerai d'entre les nations, et je les réunirai de toutes les contrées, et je les ferai rentrer dans leur terre, et je les ferai paître sur la montagne d'Israël, et dans tous les vallons et dans tous les lieux habités de leur héritage.
14 Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
Je les ferai paître en un bon pâturage, sur la haute montagne d'Israël; et c'est là que seront leurs bergeries; et elles y dormiront, et elles s'y reposeront dans les délices, et elles iront paître en un gras pâturage, sur les montagnes d'Israël.
15 Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Moi-même je ferai paître mes brebis; je leur donnerai moi-même le repos; et elles sauront que je suis le Seigneur Maître. Voici ce que dit le Seigneur Maître:
16 Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
Je chercherai celle qui sera perdue; je ramènerai celle qui sera égarée; j'entourerai de bandes celle qui sera blessée; je fortifierai les faibles; je veillerai sur les fortes, et je les ferai paître selon la justice.
17 “‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
Et vous, brebis, dit le Seigneur Maître, voilà que je distinguerai entre brebis et brebis, entre boucs et béliers.
18 Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
Ne vous suffisait-il pas de brouter un bon pâturage? Pourquoi fouler aux pieds le reste de votre pâturage? Ne vous suffisait-il pas de boire de l'eau paisible? Pourquoi troubler encore de vos pieds ce que vous n'aviez pas bu?
19 Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
Mes autres brebis n'ont-elles pas brouté l'herbe que vos pieds avaient foulée? N'ont-elles pas bu l'eau que vous aviez troublée?
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur Maître: Je distinguerai entre les brebis fortes et les brebis faibles.
21 Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
Vous heurtiez de vos flancs et de vos épaules, vous frappiez de vos cornes, vous opprimiez toute brebis faible.
22 zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
Et moi je sauverai mes brebis, et elles ne seront plus une proie, et je jugerai entre bélier et bélier.
23 Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
Et je susciterai pour eux un seul pasteur, et il les fera paître; je susciterai mon serviteur David, et il sera leur pasteur.
24 Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
Et moi, le Seigneur, je serai leur Dieu, et David, au milieu d'eux, sera leur roi. Moi, le Seigneur, j'ai parlé.
25 “‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
Et je ferai avec David une alliance de paix, et je ferai disparaître de la terre les bêtes malfaisantes, et l'on habitera le désert, et l'on dormira dans les forêts.
26 Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
Et je donnerai à mes brebis tout le contour de ma montagne; et je leur donnerai de la pluie, une pluie de bénédiction.
27 Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
Et les terres des champs produiront leurs fruits; et la terre aura toute sa fertilité; et mes brebis habiteront leur héritage dans l'espérance de la paix; et elles sauront que je suis le Seigneur quand j'aurai brisé leur joug, et que je les aurai retirées des mains de ceux qui les ont asservies.
28 Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
Et elles ne seront plus livrées en proie aux nations; et les bêtes fauves ne les dévoreront plus, et elles habiteront leur héritage dans l'espérance, et nul ne les épouvantera plus.
29 Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
Et je ferai naître pour elles une plante de paix, et elles ne périront plus par la famine sur la terre, et elles ne subiront plus les outrages des nations.
30 Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Et elles sauront que je suis le Seigneur leur Dieu, et qu'elles sont mon peuple. Maison d'Israël, dit le Seigneur Maître,
31 Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
Vous êtes mes brebis, les brebis de mon troupeau; et je suis votre Dieu, dit le Seigneur Maître.