< Ezekiyel 32 >
1 A shekara ta goma sha biyu, a wata na goma sha biyu a rana ta fari, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it was in two [plus] ten year in two [plus] ten month on [day] one of the month it came [the] word of Yahweh to me saying.
2 “Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir’auna sarkin Masar ka faɗa masa. “‘Kai kamar zaki ne a cikin al’ummai; kai kamar dodon ruwa a cikin tekuna kana ɓullowa cikin rafuffukanka, kana gurɓata ruwa da ƙafafunka kana kuma dama rafuffuka.
O son of humankind take up a lamentation on Pharaoh [the] king of Egypt and you will say to him a young lion of nations you became like and you [were] like sea monster in the seas and you burst forth in rivers your and you made turbid waters with feet your and you fouled rivers their.
3 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Da taron jama’a masu yawa zan jefa abin kamun kifi a kanka, za su kuwa jawo ka da abin kamun kifi.
Thus he says [the] Lord Yahweh and I will spread over you net my by a company of peoples many and they will bring up you in net my.
4 Zan jefar da kai a ƙasa zan jefa ka a fili. Zan sa dukan tsuntsayen sararin sama su zauna a kanka dukan namun jeji na duniya kuma za su ƙosar da kansu a kanka.
And I will abandon you on the land on [the] surface of the field I will throw you and I will cause to settle on you every bird of the heavens and I will satisfy from you [the] animal[s] of all the earth.
5 Zan baza namanka a kan duwatsu in kuma cika kwaruruka da gawarka.
And I will put flesh your on the mountains and I will fill the valleys height your.
6 Zan jiƙa ƙasar da jininka mai gudu har zuwa duwatsu, magudanan ruwa za su cika da namanka.
And I will make drink [the] land outflow your from blood your to the mountains and ravines they will be filled! from you.
7 Sa’ad da na shafe ka, zan rufe sammai in duhunta taurarinsu; zan rufe rana da girgije, wata kuwa ba zai ba da haskensa ba.
And I will cover when extinguishing you heavens and I will darken stars their [the] sun with cloud I will cover it and [the] moon not it will give light light its.
8 Dukan haskokin sammai za su zama duhu a kanka; zan kawo duhu a kan ƙasarka, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
All [the] luminaries of light in the heavens I will darken them over you and I will put darkness over land your [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
9 Zan dami zukatan mutane masu yawa sa’ad da na kawo maka hallaka a cikin al’ummai, a cikin ƙasashen da ba ka taɓa sani ba.
And I will disturb [the] heart of peoples many when bring I breaking your among the nations to lands which not you have known them.
10 Zan sa mutane da yawa su giggice saboda abin da ya same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa’ad da na kaɗa takobina a gabansu. A ranar fāɗuwarka kowannensu zai yi rawar jiki a kowane lokaci saboda ransa.
And I will make appalled on you peoples many and kings their they will shudder on you shuddering when brandish I sword my on faces their and they will tremble to moments everyone for life his on [the] day of downfall your.
11 “‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Takobin sarkin Babilon zai auko maka.
For thus he says [the] Lord Yahweh [the] sword of [the] king of Babylon it will come to you.
12 Zan sa jama’arka su mutu ta wurin takuban ƙarfafan mutane, masu bantsoro na dukan al’ummai. Za su lalatar da girman kan Masar, su kuma tumɓuke dukan jama’arta.
By [the] swords of warriors I will make fall multitude your ruthless [ones] of nations all of them and they will devastate [the] pride of Egypt and it will be destroyed all multitude its.
13 Zan hallaka dukan dabbobinta da suke kusa da ruwaye masu yawa ƙafar mutum ba zai ƙara damunsa ko kofaton dabba ya gurɓata shi.
And I will destroy all livestock its from at waters many and not it will make turbid them a foot of a human again and hooves of livestock not it will make turbid them.
14 Sa’an nan zan sa ruwanta su kwanta in sa rafuffukanta su gudu kamar mai, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Then I will make settle waters their and rivers their like oil I will make go [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
15 Sa’ad da na mai da Masar kufai na kuma raba ƙasar da abin da take cike da shi, sa’ad da na bugi dukan waɗanda suke cikinta, a sa’an nan ne za su san cewa ni ne Ubangiji.’
When make I [the] land of Egypt a desolation and [is] made desolate [the] land from fullness its when strike down I all [the] inhabitants in it and they will know that I [am] Yahweh.
16 “Wannan ne makokin da za a yi mata.’Yan matan al’ummai za su rera shi; gama Masar da dukan jama’arta za su rera shi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
[is] a lamentation It and people will chant it [the] daughters of the nations they will chant it over Egypt and over all multitude its they will chant it [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
17 A shekara ta goma sha biyu, a rana ta goma sha biyar ga wata, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And it was in two [plus] ten year on [day] fif-teen of the month it came [the] word of Yahweh to me saying.
18 “Ɗan mutum, yi kuka saboda jama’ar Masar ka kuma tura ta da’yan matan manyan al’ummai zuwa ƙarƙashin ƙasa, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
O son of humankind wail on [the] multitude of Egypt and bring down it it and [the] daughters of nations mighty to [the] earth of [the] lowest parts with [those who] go down of [the] pit.
19 Ka ce, ‘Kin fi sauran tagomashi ne? Ki gangara, ki kwanta cikin marasa kaciya.’
More than whom? are you lovely go down! and be laid! with uncircumcised [men].
20 Za su fāɗi cikin waɗanda aka kashe da takobi. Takobin da an zāre; bari a ja ta a tafi tare da dukan jama’arta.
In among [those] slain of a sword they will fall a sword it has been appointed they have drawn down it and all multitudes its.
21 Daga cikin kabari manyan shugabanni za su yi maganar Masar da abokanta su ce, ‘Sun gangara sun kuma kwanta da marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.’ (Sheol )
They will speak to him [the] leaders of [the] mighty [ones] from [the] midst of Sheol with helpers his they have come down they have lain down the uncircumcised [men] [those] slain of a sword. (Sheol )
22 “Assuriya tana can tare da dukan sojojinta; an kewaye ta da kaburburan dukan waɗanda aka kashe, dukan waɗanda suka mutu ta wurin takobi.
[is] there Assyria and all company its [are] around it graves its all of them [are] slain those [who] have fallen by the sword.
23 Kaburburansu suna cikin zurfafan rami kuma sojojinta suna kwance kewaye da kabarinta. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun mutu, an kashe su da takobi.
Which they have been put graves its in [the] remotest parts of [the] pit and it was company its around grave its all of them [are] slain [those who] have fallen by the sword who they had put terror in [the] land of [the] living.
24 “Elam tana can, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu sun mutu, an kashe su da takobi. Dukan waɗanda suka haddasa tsoro a ƙasar masu rai sun gangara wurin marasa kaciya a duniyar da take ƙarƙashi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
[is] there Elam and all multitude its around grave its all of them [are] slain those [who] have fallen by the sword who they have gone down uncircumcised - into [the] earth of [the] lowest parts who they had put terror their in [the] land of [the] living and they have borne disgrace their with [those who] go down of [the] pit.
25 An yi mata gado a cikin matattu, tare da dukan jama’arta kewaye da kabarinta. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi. Domin tsoronsu ya bazu cikin ƙasar masu rai, suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami; an kwantar da su tare da waɗanda aka kashe.
In among [those] slain people have made a bed for it among all multitude its [are] around it graves its all of them [are] uncircumcised [those] slain of a sword for it was put terror their in [the] land of [the] living and they have borne disgrace their with [those who] go down of [the] pit in among [those] slain it was made.
26 “Meshek da Tubal suna can, tare da dukan jama’arsu kewaye da kaburburansu. Dukansu marasa kaciya ne, da aka kashe da takobi domin sun haddasa tsoronsu a ƙasar masu rai.
[is] there Meshech Tubal and all multitude its [are] around it graves its all of them [are] uncircumcised pierced of [the] sword for they had put terror their in [the] land of [the] living.
27 Ba sun kwanta tare da sauran jarumawa marasa kaciyan da aka kashe, waɗanda suka gangara kabari tare da makaman yaƙinsu, waɗanda aka yi musu matashin kai da takubansu ba? Hukuncin zunubansu yana a bisa ƙasusuwansu, ko da yake tsoron waɗannan jarumawa ya manne cikin ƙasar masu rai. (Sheol )
And not they lie with warriors fallen from uncircumcised [men] who they went down Sheol with [the] weapons of war their and people put swords their under heads their and it was iniquities their on bones their for terror of warriors [was] in [the] land of [the] living. (Sheol )
28 “Kai kuma, ya Fir’auna, za a kakkarye ka za ka kuma kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi.
And you in among uncircumcised [men] you will be broken and you may lie with [those] slain of a sword.
29 “Edom tana can, sarakunanta da dukan yerimanta; duk da ikonsu, sun kwanta tare da waɗanda aka kashe da takobi. Suna kwance tare da marasa kaciya, tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
[is] there Edom kings its and all princes its who they have been put in strength their with [those] slain of a sword they with uncircumcised [men] they will lie and with [those who] go down of [the] pit.
30 “Dukan yerima arewa da dukan Sidoniyawa suna can; sun gangara tare da waɗanda aka kashe cikin kunya duk da tsoron da suka haddasa ta wurin ikonsu. Sun kwanta tare da marasa kaciya tare da waɗanda aka kashe da takobi suna kuma shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa rami.
[are] there Princes of [the] north all of them and all [the] Sidonian[s] who they have gone down with [those] slain in terror their (from strength their *LA(bh)*) being ashamed and they lay uncircumcised with [those] slain of a sword and they have borne disgrace their with [those who] go down of [the] pit.
31 “Fir’auna, shi da dukan sojojinsa, za su gan su zai kuma ta’azantu domin dukan jama’arsa da aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Them he will see Pharaoh and he will be comforted on all (multitude his *Q(K)*) [those] slain of a sword Pharaoh and all army his [the] utterance of [the] Lord Yahweh.
32 Ko da yake na sa ta haddasa tsoro a ƙasar masu rai, Fir’auna da dukan jama’arsa za su kwanta a cikin marasa kaciya, tare da waɗanda aka kashe da takobi, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
That I had put (terror my *Q(K)*) in [the] land of [the] living and he will be laid in among uncircumcised [men] with [those] slain of a sword Pharaoh and all (multitude his *Q(K)*) [the] utterance of [the] Lord Yahweh.