< Ezekiyel 28 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
耶和华的话又临到我说:
2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mai mulkin Taya cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Cikin alfarmar zuciyarka ka ce, “Ni allah ne; ina zama a kan kursiyin allah a tsakiyar tekuna.” Amma kai mutum ne ba allah ba, ko da yake ka ɗauka kana da hikima kamar allah.
“人子啊,你对泰尔君王说,主耶和华如此说: 因你心里高傲,说:我是神; 我在海中坐神之位。 你虽然居心自比神, 也不过是人,并不是神!
3 Ka fi Daniyel hikima ne? Ba asirin da yake ɓoye a gare ka?
看哪,你比但以理更有智慧, 什么秘事都不能向你隐藏。
4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka sami dukiya wa kanka ka kuma tara zinariya da azurfa cikin wuraren ajiyarka.
你靠自己的智慧聪明得了金银财宝, 收入库中。
5 Ta wurin dabararka mai girma cikin kasuwanci ka ƙara dukiyarka, kuma saboda dukiyarka zuciyarka ta cika da alfarma.
你靠自己的大智慧和贸易增添资财, 又因资财心里高傲。
6 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Domin ka ɗauka kai mai hikima ne, mai hikima kamar allah,
所以主耶和华如此说: 因你居心自比神,
7 zan kawo baƙi a kanka, waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al’ummai; za su zāre takubansu a kan kyakkyawar hikimarka su kuma ɓarke darajarka mai walƙiya.
我必使外邦人, 就是列国中的强暴人临到你这里; 他们必拔刀砍坏你用智慧得来的美物, 亵渎你的荣光。
8 Za su jefar da kai cikin rami, za ka kuwa yi muguwar mutuwa a tsakiyar tekuna.
他们必使你下坑; 你必死在海中, 与被杀的人一样。
9 Za ka iya ce yanzu, “Ni allah ne,” a gaban waɗanda suka kashe ka? Za ka zama mutum kurum, ba allah ba, a hannuwan waɗanda suka kashe ka.
在杀你的人面前你还能说“我是神”吗? 其实你在杀害你的人手中, 不过是人,并不是神。
10 Za ka yi mutuwar marar kaciya a hannuwan baƙi. Na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
你必死在外邦人手中, 与未受割礼的人一样, 因为这是主耶和华说的。”
11 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
耶和华的话临到我说:
12 “Ɗan mutum, ka yi makoki domin sarkin Taya ka kuma ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka kasance hatimin cikakke, cike da hikima da cikakke a kyau.
“人子啊,你为泰尔王作起哀歌,说主耶和华如此说: 你无所不备, 智慧充足,全然美丽。
13 Ka kasance a Eden, a lambun Allah; aka yi maka ado da kowane dutse mai daraja, yakutu, tofaz, da zumurrudu, kirisolit, onis da yasfa, saffaya, turkuwoyis da beril. Tsare-tsare da shirye-shiryenka an yi su da zinariya ne; a ranar da aka halicce ka an shirya su.
你曾在伊甸 神的园中, 佩戴各样宝石, 就是红宝石、红璧玺、金钢石、 水苍玉、红玛瑙、碧玉、 蓝宝石、绿宝石、红玉,和黄金; 又有精美的鼓笛在你那里, 都是在你受造之日预备齐全的。
14 An shafe ka kamar kerub mai tsaro, gama haka na naɗa ka. Kana a tsattsarkan dutsen Allah; ka yi tafiya a tsakiyar duwatsun wuta.
你是那受膏遮掩约柜的基路伯; 我将你安置在 神的圣山上; 你在发光如火的宝石中间往来。
15 Ka kasance marar laifi cikin dukan hanyoyinka daga ranar da aka halicce ka sai da aka sami mugunta a cikinka.
你从受造之日所行的都完全, 后来在你中间又察出不义。
16 Ta wurin yawan kasuwancinka ka cika da rikici, ka kuma yi zunubi. Saboda haka na kore ka da kunya daga dutsen Allah, na kore ka, ya kerub mai tsaro, daga cikin duwatsun wuta.
因你贸易很多, 就被强暴的事充满,以致犯罪, 所以我因你亵渎圣地, 就从 神的山驱逐你。 遮掩约柜的基路伯啊, 我已将你从发光如火的宝石中除灭。
17 Zuciyarka ta cika da alfarma saboda kyanka, ka kuma lalace hikimarka saboda darajarka. Saboda haka na jefar da kai zuwa ƙasa; na sa ka zama abin kallo a gaban sarakuna.
你因美丽心中高傲, 又因荣光败坏智慧, 我已将你摔倒在地, 使你倒在君王面前, 好叫他们目睹眼见。
18 Ta wurin yawan zunubanka da kasuwancinka na cuta ka ƙazantar da wuri mai tsarkinka. Saboda haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suke kallonka.
你因罪孽众多, 贸易不公, 就亵渎你那里的圣所。 故此,我使火从你中间发出,烧灭你, 使你在所有观看的人眼前变为地上的炉灰。
19 Dukan al’umman da suka san ka sun giggice saboda masifar da ta auko maka; ka zo ga mummunar ƙarshe ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’”
各国民中,凡认识你的, 都必为你惊奇。 你令人惊恐, 不再存留于世,直到永远。”
20 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
耶和华的话临到我说:
21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon; ka yi annabci a kanta
“人子啊,你要向西顿预言攻击她,
22 ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da ke, ya Sidon, zan sami ɗaukaka a cikinki. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na zartar da hukunci a kanta na kuma nuna kaina mai tsarki a cikinta.
说主耶和华如此说: 西顿哪,我与你为敌, 我必在你中间得荣耀。 我在你中间施行审判、显为圣的时候, 人就知道我是耶和华。
23 Zan aika da annoba a kanta in kuma sa jini ya zuba a titunanta. Kisassu za su fāɗi a cikinta, da takobi yana gāba da ita a kowane gefe. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.
我必使瘟疫进入西顿, 使血流在她街上。 被杀的必在其中仆倒, 四围有刀剑临到她, 人就知道我是耶和华。”
24 “‘Mutanen Isra’ila ba za su ƙara kasance da mugayen maƙwabta waɗanda za su zama sarƙaƙƙiya masu zafi da ƙaya mai tsini ba. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
“四围恨恶以色列家的人,必不再向他们作刺人的荆棘,伤人的蒺藜,人就知道我是主耶和华。”
25 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa sa’ad da na tattara mutanen Isra’ila daga al’ummai inda suke a warwatse, zan nuna kaina mai tsarki a cikinsu a idon al’ummai. Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu, wadda na ba wa bawana Yaƙub.
主耶和华如此说:“我将分散在万民中的以色列家招聚回来,向他们在列邦人眼前显为圣的时候,他们就在我赐给我仆人雅各之地,仍然居住。
26 Za su zauna a can lafiya su kuma gina gidaje su nome gonakin inabi; za su zauna lafiya sa’ad da zan zartar da hukunci a kan dukan maƙwabtansu da suka wulaƙanta su. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.’”
他们要在这地上安然居住。我向四围恨恶他们的众人施行审判以后,他们要盖造房屋,栽种葡萄园,安然居住,就知道我是耶和华—他们的 神。”

< Ezekiyel 28 >