< Ezekiyel 25 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And there is a word of YHWH to me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa ka kuma yi annabci a kansu.
“Son of man, set your face toward the sons of Ammon, and prophesy against them;
3 Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun ce “Yauwa” a kan wuri mai tsarkina sa’ad da aka ƙazantar da shi da kuma a kan ƙasar Isra’ila sa’ad da aka mai da ita kufai da lokacin da aka kai mutanen Yahuda bautar talala,
and you have said to the sons of Ammon: Hear a word of Lord YHWH! Thus said Lord YHWH: Because of your saying, Aha, to My sanctuary, Because it has been defiled, And to the ground of Israel, Because it has been desolate, And to the house of Judah, Because they have gone into a removal:
4 saboda haka zan ba da ku ga mutanen Gabas abin mallaka. Za su kafa sansanoninsu su yi tentunansu a cikinku; za su ci’ya’yan itatuwanku su kuma sha madararku.
Therefore, behold, I am giving you to sons of the east for a possession, And they set their towers in you, And have placed their dwelling places in you. They eat your fruit, and they drink your milk,
5 Zan mai da Rabba wurin kiwo don raƙuma, Ammon kuma wurin hutu don tumaki. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
And I have given Rabbah for a habitation of camels, And the sons of Ammon for the crouching of a flock, And you have known that I [am] YHWH.
6 Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin kun tafa hannuwanku kuka kuma buga ƙafafunku, kuna farin ciki don nuna dukan ƙiyayyarku a kan ƙasar Isra’ila,
For thus said Lord YHWH: Because of your clapping the hand, And of your stamping with the foot, And you rejoice with all your despite in soul Against the ground of Israel,
7 saboda haka zan miƙa hannuna gāba da ku in kuma ba da ku ganima ga al’ummai. Zan datse ku daga al’ummai in kuma kore ku daga ƙasashe. Zan hallaka ku, za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji.’”
Therefore, behold, I have stretched out My hand against you, And have given you for a portion to nations, And I have cut you off from the peoples, And caused you to perish from the lands; I destroy you, and you have known that I [am] YHWH.
8 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Mowab da Seyir sun ce, “Duba, gidan Yahuda ta zama sauran al’ummai,”
Thus said Lord YHWH: Because of the saying of Moab and Seir: Behold, the house of Judah [is] as all the nations;
9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab, farawa daga garuruwan da suke kan iyaka, Bet-Yeshimot, Ba’al-Meyon da Kiriyatayim, darajar ƙasar.
Therefore, behold, I am opening the shoulder of Moab—From the cities—from his cities—from his frontier, The beauty of the land, Beth-Jeshimoth, Ba‘al-Meon, and Kiriathaim,
10 Zan ba da Mowabawa tare da Ammonawa ga mutanen Gabas abin mallaka, don kada a ƙara tuna da Ammonawa a cikin al’ummai;
To the sons of the east, with the sons of Ammon, And I have given it for a possession, So that the sons of Ammon are not remembered among nations.
11 zan hukunta Mowabawa. Ta haka za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
And I do judgments in Moab, And they have known that I [am] YHWH.
12 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Edom ya ɗauki wa kanta fansa a kan gida Yahuda, ta yi babban laifi ta wurin yin haka,
Thus said Lord YHWH: Because of the doings of Edom, In taking vengeance on the house of Judah, Indeed, they are very guilty, And they have taken vengeance on them.
13 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan miƙa hannuna a kan Edom in kashe mutanenta da dabbobinsu. Zan sa ta zama kufai, kuma tun daga Teman har zuwa Dedan za a kashe su da takobi.
Therefore, thus said Lord YHWH: I have stretched out My hand against Edom, And I have cut off man and beast from it, And given it up—a ruin, from Teman even to Dedan, They fall by sword.
14 Zan ɗau fansa a kan Edom ta hannun mutanena Isra’ila, za su kuwa hukunta Edom bisa ga fushina da hasalata; za su san sakayyata, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
And I have given My vengeance on Edom, By the hand of My people Israel, And they have done in Edom, According to My anger, and according to My fury, And they have known My vengeance, A declaration of Lord YHWH.
15 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin Filistiyawa sun yi sakayya, suka ɗauki fansa da mugunta a zukatansu, da kuma daɗaɗɗen ƙiyayya sun nemi su hallaka Yahuda,
Thus said Lord YHWH: Because of the doings of the Philistines in vengeance, And they take vengeance with despite in soul, Destruction [with] continuous enmity,
16 saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da miƙa hannuna a kan Filistiyawa, zan kuwa datse Keretawa in kuma hallaka waɗanda suka rage a bakin teku.
Therefore, thus said Lord YHWH: Behold, I am stretching out My hand against the Philistines, And I have cut off the Cherethim, And destroyed the remnant of the haven of the sea,
17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani cikin hasalata. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na ɗauki fansa a kansu.’”
And done great vengeance on them with furious reproofs, And they have known that I [am] YHWH, In My giving out My vengeance on them!”

< Ezekiyel 25 >