< Ezekiyel 24 >

1 A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
The word of Yahweh came to me in the ninth year, in the tenth month, and on the tenth day of the month, saying,
2 “Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
“Son of man, write for yourself the name of this day, this exact day, for this exact day the king of Babylon has besieged Jerusalem.
3 Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
So speak a proverb against this rebellious house, a parable. Say to them, 'The Lord Yahweh says this: Place the cooking pot. Place it and pour water into it.
4 Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
Gather pieces of food within it, every good piece—the thigh and shoulder— and fill it with the best bones.
5 ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
Take the best of the flock and pile up the bones under it. Bring it to a boil and cook the bones in it.
6 “‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
Therefore the Lord Yahweh says this: Woe to the city of blood, a cooking pot that has rust in it and that rust will not come out of it. Take piece after piece from it, but do not cast lots for it.
7 “‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
For her blood is in the midst of her. She has set it on the smooth rock; she has not poured it out on the ground to cover it with dust,
8 Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
so it brings fury up to exact vengeance. I placed her blood on the smooth rock so it could not be covered.
9 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
Therefore, the Lord Yahweh says this: Woe to the city of blood. I will also enlarge the pile of wood.
10 Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
Stack up the wood and kindle the fire. Cook the meat well and mix in the spices and let the bones be charred.
11 Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
Then set the pot on its coals empty, in order to heat and scorch its bronze, so its uncleanness within it will be melted, its corrosion consumed.'
12 Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
She has become weary because of toil, but her corrosion has not gone out of her by the fire.
13 “‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
Your shameful behavior is in your uncleanness. Because I tried to cleanse you but still you would not be cleansed from your uncleanness, you will not be cleansed anymore until I have satisfied my fury upon you.
14 “‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
I, Yahweh, have declared it, and I will do it. I will not relent nor will I rest from it. As your ways were, and as your activities, they will judge you!—this is the Lord Yahweh's declaration.”
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Then the word of Yahweh came to me, saying,
16 “Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
“Son of man! Behold, I am taking the desire of your eyes from you with a plague, but you must not mourn nor weep, and your tears must not flow.
17 Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
You must groan silently. Do not conduct a funeral for the dead. Tie your turban on you and place your sandals on your feet, but do not veil your facial hair or eat the bread of men who mourn for having lost their wives.”
18 Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
So I spoke to the people in the morning, and my wife died in the evening. In the morning I did what I had been commanded to do.
19 Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
The people asked me, “Will you not tell us what these things mean, the things that you are doing?”
20 Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
So I said to them, “The word of Yahweh came to me, saying,
21 faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
'Say to the house of Israel, the Lord Yahweh says this: Behold! I will desecrate my sanctuary—the pride of your power, the delight of your eyes, and the yearning of your soul, and your sons and your daughters whom you left behind will fall by the sword.
22 Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
Then you will do exactly as I have done: you will not veil your facial hair, nor eat the bread of mourning men!
23 Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
Instead, your turbans will be on your heads, and your sandals on your feet; you will not mourn nor weep, for you will melt away in your iniquities, and each man will groan for his brother.
24 Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
So Ezekiel will be a sign for you, as everything that he has done you will do when this comes. Then you will know that I am the Lord Yahweh!'”
25 “Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
“But you, son of man, on the day that I capture their temple, which is their joy, their pride, and what they see and desire—and when I take away their sons and daughters—
26 a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
on that day, a refugee will come to you to give you the news!
27 A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”
On that day your mouth will be opened up to that refugee and you will speak—you will no longer be silent. You will be a sign for them so that they will know that I am Yahweh.”

< Ezekiyel 24 >