< Ezekiyel 24 >

1 A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And there is a word of YHWH to me, in the ninth year, in the tenth month, on the tenth of the month, saying,
2 “Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
“Son of man, write! Write the name of the day for yourself, this very day; the king of Babylon has leaned toward Jerusalem in this very day.
3 Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
And use an allegory toward the house of rebellion, and you have said to them, Thus said Lord YHWH: To set on the pot, to set [it] on, and also to pour water into it,
4 Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
To gather its pieces to it, every good piece, Thigh and shoulder, to fill in the choice of the bones.
5 ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
To take the choice of the flock, And also to pile the bones under it, Boil it thoroughly, indeed, cook its bones in its midst.
6 “‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
Therefore, thus said Lord YHWH: Woe [to] the city of blood, A pot whose scum [is] in it, And its scum has not come out of it, By piece of it, by piece of it bring it out, a lot has not fallen on it.
7 “‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
For her blood has been in her midst, She has set it on a clear place of a rock, She has not poured it on the earth, To cover it over with dust.
8 Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
To cause fury to come up to take vengeance, I have put her blood on a clear place of a rock—not to be covered.
9 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
Therefore, thus said Lord YHWH: Woe [to] the city of blood, indeed, I make the pile great.
10 Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
Make the wood abundant, Kindle the fire, consume the flesh, And make the compound, And let the bones be burned.
11 Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
And cause it to stand empty on its coals, So that its bronze is hot and burning, Its uncleanness has been melted in its midst, Its scum is consumed.
12 Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
She has wearied herself [with] sorrows, And the abundance of her scum does not go out of her, Her scum [is] in the fire.
13 “‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
Wickedness [is] in your uncleanness, Because I have cleansed you, And you have not been cleansed, You are not cleansed from your uncleanness again, Until I have caused My fury to rest on you.
14 “‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
I, YHWH, have spoken, It has come, and I have done [it], I do not free, nor do I spare, nor do I regret, According to your ways, and according to your acts, They have judged you, A declaration of Lord YHWH.”
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And there is a word of YHWH to me, saying,
16 “Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
“Son of man, behold, I am taking the desire of your eyes from you by a stroke, and you do not mourn, nor weep, nor let your tear come.
17 Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
Cease to groan [and] make no mourning [for] the dead, bind your headdress on yourself, and put your shoes on your feet, and you do not cover over the upper lip, and you do not eat [the] bread of men.”
18 Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
And I speak to the people in the morning, and my wife dies in the evening, and I do in the morning as I have been commanded.
19 Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
And the people say to me, “Do you not declare to us what these [are] to us, that you are doing?”
20 Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
And I say to them, “A word of YHWH has been to me, saying,
21 faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
Say to the house of Israel, Thus said Lord YHWH: Behold, I am defiling My sanctuary, The excellence of your strength, The desire of your eyes, and the pitied of your soul, And your sons and your daughters whom you have left, fall by sword.
22 Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
And you have done as I have done, You have not covered over the upper lip, And you do not eat [the] bread of men.
23 Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
And your headdresses [are] on your heads, And your shoes [are] on your feet, You do not mourn nor do you weep, And you have wasted away for your iniquities, And you have howled to one another.
24 Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
And Ezekiel has been for a type to you; according to all that he has done you do. In its coming in—you have known that I [am] Lord YHWH.”
25 “Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
“And you, son of man, is it not in the day of My taking from them their strength, the joy of their beauty, the desire of their eyes, and the song of their soul—their sons and their daughters?
26 a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
In that day the escaped one comes to you to cause the ears to hear.
27 A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”
In that day your mouth is opened with the escaped and you speak, and are not silent anymore, and you have been for a type to them, and they have known that I [am] YHWH.”

< Ezekiyel 24 >