< Ezekiyel 24 >
1 A shekara ta tara, a wata na goma, a rana ta goma, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Again in the ninth yeere, in the tenth moneth, in the tenth day of the moneth, came the worde of the Lord vnto me, saying,
2 “Ɗan mutum, ka rubuta wannan rana, wannan rana, domin sarkin Babilon ya yi ƙawanya wa Urushalima a wannan rana.
Sonne of man, write thee the name of the day, euen of this same day: for the King of Babel set himselfe against Ierusalem this same day.
3 Ka faɗa wa wannan gidan’yan tawaye wani misali ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ka sa tukunyar dahuwa; ka sa ta a kan wuta ka kuma zuba ruwa a cikinta.
Therefore speake a parable vnto the rebellious house, and say vnto them, Thus sayth the Lord God, Prepare a pot, prepare it, and also powre water into it.
4 Ka sa gunduwoyin nama a cikinta dukan gunduwoyi masu kyau, cinya da kafaɗa. Ka cika ta da waɗannan ƙasusuwa mafi kyau;
Gather the pieces thereof into it, euen euery good piece, as the thigh and the shoulder, and fill it with the chiefe bones.
5 ka kama mafi kyau daga cikin garken. Ka tara itace a ƙarƙashinta saboda ƙasusuwan; ka sa ta tafasa ka kuma dafa ƙasusuwan a cikinta.
Take one of the best sheepe, and burne also the bones vnder it, and make it boyle well, and seethe the bones of it therein,
6 “‘Gama wannan shi ne abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini, ga tukunya wadda take da tsatsa, wadda tsatsarta ba za tă fita ba! Ka fitar da shi gunduwa-gunduwa ba tare da jefa ƙuri’a a kansu ba.
Because the Lord God sayth thus, Woe to the bloody citie, euen to the pot, whose skomme is therein, and whose skomme is not gone out of it: bring it out piece by piece: let no lot fall vpon it.
7 “‘Gama zubar da jini yana a tsakiyarta, ta zubar da shi a dutsen da yake a fili; ba tă zubar da shi a ƙasa ba, inda ƙura za tă rufe shi.
For her blood is in the middes of her: shee set it vpon an high rocke, and powred it not vpon on the ground to couer it with dust,
8 Don a zuga hasala a kuma yi sakayya na sa jininta a dutsen da ba a rufe ba, saboda kada a rufe.
That it might cause wrath to arise, and take vengeance: euen I haue set her blood vpon an high rocke that it should not be couered.
9 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Kaito birnin nan mai zubar da jini! Ni ma zan jibge itace da yawa.
Therefore thus saith ye Lord God, Woe to the bloody citie, for I will make ye burning great.
10 Ka tula gumagumai ka kuma ƙuna wuta. Ka dafa naman da kyau, kana haɗawa da yaji; ka kuma bar ƙasusuwan su ƙone.
Heape on much wood: kindle the fire, consume the flesh, and cast in spice, and let the bones be burnt.
11 Sa’an nan ka sa tukunyan nan da babu kome a kan garwashi sai ta yi zafi har darmarta ta yi ja wur domin dattinta ya narke tsatsarta kuma ta ƙone.
Then set it emptie vpon the coles thereof, that the brasse of it may be hot, and may burne, and that the filthinesse of it may be molten in it, and that the skomme of it may be consumed.
12 Ta gajiyar da dukan ƙoƙari; ba a fid da tsatsarta nan mai yawa ba, kai, ko a wuta ma.
She hath wearied her selfe with lyes, and her great skomme went not out of her: therefore her skomme shall be consumed with fire.
13 “‘Yanzu ƙazantarki ita ce lalaci. Domin na yi ƙoƙari in tsabtacce ke amma ba ki tsabtattu daga ƙazantarki ba, ba za ki ƙara yin tsabta ba sai hasalata a kanki ya kwanta.
Thou remainest in thy filthines and wickednes: because I would haue purged thee, and thou wast not purged, thou shalt not be purged from thy filthines, till I haue caused my wrath to light vpon thee.
14 “‘Ni Ubangiji na faɗa. Lokaci ya zo da zan aikata. Ba zan janye ba; ba zan ji tausayi ba, ba kuwa zan bari ba. Za a hukunta ki bisa ga hali da ayyukanki, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
I the Lord haue spoken it: it shall come to passe, and I will doe it: I will not goe backe, neither will I spare, neither will I repent: according to thy wayes, and according to thy workes shall they iudge thee, sayeth the Lord God.
15 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Also the worde of ye Lord came vnto me, saying,
16 “Ɗan mutum, da farat ɗaya ina gab da ɗauke abin da idanunka suke jin daɗin gani. Duk da haka kada ka yi makoki ko ka yi kuka ko ka zub da hawaye.
Sonne of man beholde, I take away from thee the pleasure of thine eyes with a plague: yet shalt thou neither mourne nor weepe, neither shall thy teares runne downe.
17 Ka yi nishi shiru; kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka ka kuma sa takalmanka a ƙafa; kada ka rufe sashen fuskarka daga ƙasa ko ka ci abincin da masu kuka sukan ci.”
Cease from sighing: make no mourning for the dead, and binde the tyre of thine head vpon thee, and put on thy shooes vpon thy feete, and couer not thy lips, and eate not the bread of men.
18 Da gari ya waye, sai na yi magana da mutane, da yamma kuwa matata ta rasu. Kashegari na yi yadda aka umarce ni.
So I spake vnto the people in the morning, and at euen my wife dyed: and I did in the morning, as I was commanded.
19 Sai mutane suka tambaye ni suka ce, “Ba za ka faɗa mana abin da waɗannan abubuwa suke nufi a gare mu ba?”
And the people said vnto me, Wilt thou not tell vs what these things meane towarde vs that thou doest so?
20 Sai na ce musu, “Maganar Ubangiji ta zo mini cewa
Then I answered them, The worde of the Lord came vnto me, saying,
21 faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da ƙazantar da wuri mai tsarkina, kagarar da kuke taƙama, abin da idanunku suke jin daɗin gani, abin faranta zuciyarku.’Ya’yanku maza da mata waɗanda kun bari a baya za su mutu ta wurin takobi.
Speake vnto the house of Israel, Thus sayth the Lord God, Behold, I will pollute my Sanctuarie, euen the pride of your power, the pleasure of your eyes, and your hearts desire, and your sonnes, and your daughters whom ye haue left, shall fall by the sworde.
22 Za ku kuma yi yadda na yi. Ba za ku rufe sashe ƙasa na fuskarku ko ku ci abinci da masu kuka sukan ci ba.
And ye shall doe as I haue done: ye shall not couer your lippes, neither shall ye eate the bread of men.
23 Za ku naɗa rawunanku a kai ku sa takalmanku a ƙafafunku. Ba za ku yi kuka ko makoki ba amma za ku lalace saboda zunubanku ku kuma yi ta yin nishi.
And your tyre shalbe vpon your heads, and your shooes vpon your feete: ye shall not mourne nor weepe, but ye shall pine away for your iniquities, and mourne one toward another.
24 Ezekiyel zai zama alama gare ku; za ku yi daidai yadda ya yi. Sa’ad da wannan ya faru, za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’
Thus Ezekiel is vnto you a signe: according to all that he hath done, ye shall do: and when this commeth, ye shall know that I am the Lord God.
25 “Kai kuma ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu kagararsu, farin cikinsu da darajarsu, abin da idanunsu ke jin daɗin gani, abin da yake faranta musu zuciya, da kuka’ya’yansu maza da mata,
Also, thou sonne of man, shall it not be in the day when I take from them their power, ye ioy of their honor, ye pleasure of their eyes, and the desire of their heart, their sonnes and their daughters?
26 a ranan nan wanda ya tsere zai zo don yă ba ka labari.
That he that escapeth in that day, shall come vnto thee to tell thee that which hee hath heard with his eares?
27 A lokacin bakinka zai buɗe, za ka yi magana da shi ba kuwa za ka ƙara yin shiru ba. Ta haka za ka zama alama gare su, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.”
In that day shall thy mouth be opened to him which is escaped, and thou shalt speake, and be no more dumme, and thou shalt be a signe vnto them, and they shall knowe that I am the Lord.