< Ezekiyel 22 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
2 “Ɗan mutum, za ka shari’anta ta? Za ka shari’anta wannan birni mai kisankai? To, sai ka kalubalance ta da dukan ayyukanta na banƙyama
" Et toi, fils de l'homme, jugeras-tu, jugeras-tu la ville de sang? Fais-lui connaître toutes ses abominations,
3 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ya birnin da take kawo wa kansa hallaka ta wurin kisankai a cikinta kina kuma ƙazantar da kanki ta wurin yin gumaka,
et dis: Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Ville qui répand le sang au dedans d'elle, pour que son temps vienne, et qui se couvre d'idoles infâmes pour se souiller!
4 kin zama mai laifi saboda jinin da kika zubar kika kuma zama ƙazantacciya ta wurin gumakan da kika yi. Kin kawo kwanakinki ga ƙarshe, kuma ƙarshen shekarunki sun zo. Saboda haka zan mai da ke abar ba’a ga al’ummai da abin dariya ga dukan ƙasashe.
Par le sang que tu as répandu, tu t'es rendue criminelle; par les idoles infâmes que tu as faites, tu t'es souillée; et tu as ainsi avancé tes jours, et tu es parvenue au terme de tes années. C'est pourquoi je t'ai rendue un objet d'opprobre pour les nations et une risée dans tous les pays.
5 Waɗanda suke kusa da waɗanda suke nesa za su yi miki ba’a, ya ke birni marar kunya, cike da rigima.
Ceux qui sont près et ceux qui sont loin de toi se moqueront de toi, souillée de réputation, grande en désordre!
6 “‘Duba yadda kowane yerima Isra’ila waɗanda suke cikinki yake yin amfani da ikonsa yana kisankai.
Voici que les princes d'Israël, chacun selon ses forces, sont occupés chez toi à répandre le sang.
7 A cikinki sun rena mahaifi da mahaifiya; a cikinki sun zalunci baƙo suka wulaƙanta maraya da gwauruwa.
Chez toi, on méprise père et mère; au milieu de toi, on maltraite l'étranger; chez toi, on opprime l'orphelin et la veuve.
8 Kin rena abubuwana masu tsarki kika kuma ƙazantar da Asabbataina.
Tu méprises mon sanctuaire et tu profanes mes sabbats.
9 A cikinki akwai mutane waɗanda suka nace su yi kisankai; a cikinki akwai waɗanda suke ci a dutsen tsafi suna yin ayyukan lalata.
Il y a chez toi des gens qui calomnient pour répandre le sang; chez toi, on mange sur les montagnes; on commet des énormités au milieu de toi.
10 A cikinki akwai waɗanda suke kwana da matan mahaifansu; a cikinki akwai waɗanda suke kwana da mata a lokacin da suke al’adarsu, sa’ad da suke da rashin tsarki.
Chez toi, on découvre la nudité de son père; chez toi, on fait violence à la femme pendant sa souillure.
11 A cikinki mutum guda yakan yi laifi abin ƙyama da matar maƙwabcinsa, wani cikin rashin kunya ya ƙazantar da matar ɗansa, wani kuma ya kwana da’yar’uwansa,’yar mahaifinsa.
L'un commet l'abomination avec la femme de son prochain, un autre souille par l'impureté sa belle-fille chez toi, un autre fait violence à sa sœur, fille de son père.
12 A cikinki mutane suna karɓan cin hanci don su yi kisankai; kina ba da rance da ruwa da ƙari, kina kuma cin riba a kan maƙwabcinki ta wurin ƙwace. Kina kuma manta da ni, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Chez toi, ou reçoit des présents pour répandre le sang; tu prends l'usure et un intérêt; tu dépouilles par la violence ton prochain; et moi, tu m'oublies, — oracle du Seigneur Yahweh.
13 “‘Tabbatacce zan tafa hannuwana a kan ƙazamar riba da kika ci da jinin da kin zubar a cikinki.
Mais voici que je frappe dans ma main à cause du gain déshonnête que tu as fait, et à cause du sang qui est au milieu de toi.
14 Ƙarfin halinki zai jure ko kuwa hannuwanki za su yi ƙarfi a ranar da na gamu da ke? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.
Ton cœur tiendra-t-il bon, tes mains seront-elles fermes aux jours où j'agirai contre toi? Moi, Yahweh, j'ai dit et j'agirai.
15 Zan watsar da ke cikin al’ummai in warwatsa ke cikin ƙasashe; zan kuma kawo ƙarshen rashin tsarkinki.
Je te disperserai parmi les nations, je te sèmerai dans les pays, et j'ôterai de toi toute ta souillure,
16 Sa’ad da ki ƙazantu a idanun al’umma, za ki san cewa ni ne Ubangiji.’”
et tu seras profanée chez toi aux yeux des nations; et tu sauras que je suis Yahweh. "
17 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
18 “Ɗan mutum, gidan Isra’ila ta zama ƙwan maƙera a gare ni; dukansu tagulla ne, kuza, ƙarfe da darma da suka rage a tanderu. Su ƙwan maƙerar azurfa ne kawai.
" Fils de l'homme, la maison d'Israël s'est changée pour moi en scories; eux tous sont de l'airain, de l'étain, du fer et du plomb au milieu du fourneau; ils sont devenus les scories de l'argent.
19 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ‘Domin ku duka kun zama ƙwan maƙera, zan tattara ku a Urushalima.
C'est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh: Parce que vous êtes tous devenus des scories, à cause de cela, voici que je vais vous rassembler au milieu de Jérusalem.
20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, tagulla, ƙarfe, darma da kuza a cikin tanderu don su narkar da su da wuta, haka zan tattara ku cikin fushina da kuma hasalata in sa ku cikin birnin in narkar da ku.
Comme ou met ensemble l'argent, l'airain, le fer, le plomb et l'étain au milieu d'un fourneau et qu'on souffle le feu sur le fourneau pour les fondre, ainsi je vous rassemblerai dans ma colère et mon courroux; je vous mettrai là et je vous fondrai.
21 Zan tattara ku zan kuma hura muku wutar hasalata, za ku kuma narke a cikinta.
Je vous rassemblerai et je soufflerai sur vous, avec le feu de ma fureur, et vous serez fondus au milieu de Jérusalem.
22 Kamar yadda azurfa kan narke a tanderu, haka za ku narke a cikinta, kuma za ku san cewa Ni Ubangiji na zubo muku da zafin fushina.’”
Comme on fond l'argent au milieu d'un fourneau, ainsi vous serez fondus au milieu d'elle; et vous saurez que moi, Yahweh, j'ai répandu mon courroux sur vous. "
23 Har yanzu maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
La parole de Yahweh me fut adressée en ces termes:
24 “Ɗan mutum, ka faɗa wa ƙasar, ‘Ke ƙasa ce marar ruwan sama ko yayyafi a ranar hasala.’
" Fils de l'homme, dis-lui: Tu es une terre qui n'a pas été purifiée, qui n'a pas été lavée par la pluie, en un jour de colère.
25 Akwai haɗin bakin sarakunanki a cikinki kamar rurin zaki mai yayyage ganimarsa; suna cin mutane, suna kwashe dukiya da abubuwa masu daraja suna mai da yawanci gwauraye a cikinki.
Il y a au milieu d'elle une conspiration de ses prophètes. Comme un lion rugissant qui déchire sa proie, ils dévorent les âmes, ils s'emparent des biens et des trésors, ils multiplient ses veuves au milieu d'elle.
26 Firistocinki suna karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana; ba sa bambanta tsakanin tsarki da marar tsarki; suna koyarwa cewa babu bambanci tsakanin marar tsarki da mai tsarki; suna kuma rufe idanunsu ga kiyaye Asabbataina, da haka suke saɓon sunana.
Ses prêtres ont violé ma loi et profané mon sanctuaire; ils ne distinguent pas entre le saint et le profane; ils n'enseignent pas la différence entre celui qui est souillé et celui qui est pur; ils ferment leurs yeux sur mes sabbats, et je suis profané au milieu d'eux.
27 Shugabanninki a cikinki suna kama da kyarketai masu yayyage ganimarsu; suna kisa suna kuma kashe mutane don samun ƙazamar riba.
Ses chefs sont au milieu d'elle comme des loups qui déchirent leur proie, répandant le sang, perdant des âmes pour faire des gains.
28 Annabawanki sun yi wa waɗannan ayyuka shafe da farar ƙasa ta wurin wahayin ƙarya da duban ƙarya. Suna cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa’ alhali kuwa Ubangiji bai faɗa ba.
Et ses prophètes leur plâtrent tous ces crimes; ils ont des visions vaines et des oracles menteurs; ils disent: " Ainsi parle le Seigneur Yahweh "; et Yahweh n'a point parlé.
29 Mutanen ƙasar na yin ƙwace suna yin fashi; suna cin zalin matalauta da mabukata suna wulaƙanta baƙo suna hana musu adalci.
Le peuple du pays commet des violences et s'adonne à la rapine; ils foulent le malheureux et l'indigent, et font violence à l'étranger sans motif.
30 “Na nemi mutum guda a cikinsu wanda zai gina katanga ya tsaya a gabana a tsakani a madadin ƙasar don kada in hallaka ta, amma ban sami ko ɗaya ba.
J'ai cherché parmi eux un homme qui fit une clôture et qui se tint à la brèche devant moi pour le pays, afin que je ne détruise pas; et je ne l'ai pas trouvé.
31 Saboda haka zan zuba hasalata a kansu in cinye su da wutar fushina, ina ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Et j'ai répandu sur eux mon courroux, et je les ai consumés par le feu de ma fureur, et j'ai fait retomber leurs œuvres sur leur tête, — oracle du Seigneur Yahweh. "

< Ezekiyel 22 >