< Ezekiyel 2 >

1 Ya ce mini, “Ɗan mutum, tashi ka tsaya a ƙafafunka zan kuma yi maka magana.”
Il me dit: " Fils de l'homme, tiens-toi sur tes pieds, et je te parlerai. "
2 Yayinda yake magana, sai Ruhu ya sauko mini ya kuma tā da ni a ƙafafuna, na kuma ji shi yana mini magana.
Et comme il me parlait, l'Esprit entra en moi et me fit tenir sur mes pieds, et j'entendis celui qui me parlait.
3 Ya ce, “Ɗan mutum, ina aikan ka zuwa ga Isra’ilawa, zuwa ga al’ummar’yan tawayen nan da suka yi mini tayarwa; su da kakanninsu sun yi mini tawaye har yă zuwa yau.
Il me dit: " Fils de l'homme, je t'envoie vers les enfants d'Israël, vers les peuples rebelles qui se sont révoltés contre moi; eux et leurs pères ont péché contre moi, même jusqu'à ce jour.
4 Mutanen da nake aikan ka masu ƙin ji ne da kuma taurinkai. Ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’
Ces fils à la face impudente et au cœur endurci, c'est vers eux que je t'envoie. Et tu leur diras: Ainsi a parlé le Seigneur Yahweh.
5 Kuma ko su ji ko kada su ji, gama su gida ne mai tawaye, za su san cewa akwai annabi a cikinsu.
Pour eux, qu'ils écoutent ou n'écoutent point — car c'est une maison de rebelles, — ils sauront qu'il y a eu un prophète au milieu d'eux.
6 Kai kuwa, ɗan mutum, kada ka ji tsoro, ko da sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa duk sun kewaye ka kana kuma zama a cikin kunamai. Kada ka ji tsoron abin da za ka faɗa ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gida ne mai tawaye.
Et toi, fils de l'homme, ne les crains pas et n'aie pas peur de leurs paroles, car tu es avec des chardons et des épines, et tu habites avec des scorpions. N'aie pas peur de leurs paroles et ne redoute pas leurs faces, car c'est une maison de rebelles.
7 Dole ka yi maganata gare su, ko su ji ko kada su ji, gama su’yan tawaye ne.
Et tu leur diras mes paroles, qu'ils écoutent ou n'écoutent pas, car ce sont des rebelles.
8 Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da zan faɗa maka. Kada ka yi tawaye kamar wannan gidan’yan tawaye; ka buɗe bakinka ka kuma ci abin da na ba ka.”
Et toi, fils de l'homme, écoute ce que je te dis: Ne sois pas rebelle comme la maison rebelle. Ouvre ta bouche et mange ce que je te donne. "
9 Sai na duba, na kuma ga hannu ya miƙe zuwa wurina. A cikinsa akwai littafi,
Je regardai, et voici qu'une main était tendue vers moi, et voici qu'elle tenait un livre roulé.
10 wanda ya nannaɗe a gabana. A kowane gefensa akwai rubutun kalmomin makoki da kuka da kuma kaito.
Il le déroula devant moi, et il était écrit en dedans et en dehors; et ce qui y était écrit était des chants de deuil, des lamentations et des plaintes.

< Ezekiyel 2 >