< Ezekiyel 2 >

1 Ya ce mini, “Ɗan mutum, tashi ka tsaya a ƙafafunka zan kuma yi maka magana.”
And he seide to me, Thou, sone of man, stonde on thi feet, and Y schal speke with thee.
2 Yayinda yake magana, sai Ruhu ya sauko mini ya kuma tā da ni a ƙafafuna, na kuma ji shi yana mini magana.
And the spirit entride in to me, after that he spak to me, and settide me on my feet. And Y herde oon spekynge to me,
3 Ya ce, “Ɗan mutum, ina aikan ka zuwa ga Isra’ilawa, zuwa ga al’ummar’yan tawayen nan da suka yi mini tayarwa; su da kakanninsu sun yi mini tawaye har yă zuwa yau.
and seiynge, Sone of man, Y sende thee to the sones of Israel, to folkis apostatas, `ether goynge a bak fro feith, that yeden awei fro me; the fadris of hem braken my couenaunt til to this dai.
4 Mutanen da nake aikan ka masu ƙin ji ne da kuma taurinkai. Ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’
And the sones ben of hard face, and of vnchastisable herte, to whiche Y sende thee. And thou schalt seie to hem, The Lord God seith these thingis;
5 Kuma ko su ji ko kada su ji, gama su gida ne mai tawaye, za su san cewa akwai annabi a cikinsu.
if perauenture nameli thei heren, and if perauenture thei resten, for it is an hous terrynge to wraththe. And thei schulen wite, that a profete is in the myddis of hem.
6 Kai kuwa, ɗan mutum, kada ka ji tsoro, ko da sarƙaƙƙiya da ƙayayyuwa duk sun kewaye ka kana kuma zama a cikin kunamai. Kada ka ji tsoron abin da za ka faɗa ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gida ne mai tawaye.
Therfore thou, sone of man, drede not hem, nether drede thou the wordis of hem; for vnbileueful men and distrieris ben with thee, and thou dwellist with scorpiouns. Drede thou not the wordis of hem, and drede thou not the faces of hem, for it is an hous terrynge to wraththe.
7 Dole ka yi maganata gare su, ko su ji ko kada su ji, gama su’yan tawaye ne.
Therfor thou schalt speke my wordis to hem, if perauenture thei heren, and resten, for thei ben terreris to wraththe.
8 Amma kai, ɗan mutum, ka saurari abin da zan faɗa maka. Kada ka yi tawaye kamar wannan gidan’yan tawaye; ka buɗe bakinka ka kuma ci abin da na ba ka.”
But thou, sone of man, here what euer thingis Y schal speke to thee; and nyle thou be a terrere to wraththe, as the hows of Israel is a terrere to wraththe. Opene thi mouth, and ete what euer thingis Y yyue to thee.
9 Sai na duba, na kuma ga hannu ya miƙe zuwa wurina. A cikinsa akwai littafi,
And Y siy, and lo! an hond was sent to me, in which a book was foldid togidere.
10 wanda ya nannaɗe a gabana. A kowane gefensa akwai rubutun kalmomin makoki da kuka da kuma kaito.
And he spredde abrood it bifor me, that was writun with ynne and with outforth. And lamentaciouns, and song, and wo, weren writun ther ynne.

< Ezekiyel 2 >