< Ezekiyel 17 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And the worde of the Lord came vnto mee, saying,
2 “Ɗan mutum, ka shirya kacici-kacici ka faɗa wa gidan Isra’ila misali.
Sonne of man, put foorth a parable and speake a prouerbe vnto the house of Israel,
3 Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa babbar gaggafa mai manyan fikafikai, dogayen gasusuwa da gasusuwa da yawa masu launi iri-iri ta zo Lebanon. Ta cire kan al’ul,
And say, Thus saith the Lord God, The great eagle with great wings, and long wings, and ful of fethers, which had diuers colours, came vnto Lebanon, and tooke the highest branch of the cedar,
4 ta karya kan tohonsa da yake can bisansa ta kai ƙasar ciniki, inda ta shuka shi a birnin’yan kasuwa.
And brake off the toppe of his twigge, and caried it into the land of marchants, and set it in a citie of marchants.
5 “‘Ta ɗebi waɗansu irin ƙasarku ta sa a ƙasa mai taƙi. Ta shuka shi kamar itacen wardi kusa da ruwa mai yawa,
Hee tooke also of the seede of the lande, and planted it in a fruitfull ground: hee placed it by great waters, and set it as a willowe tree.
6 ya kuwa yi toho ya zama kuringa gajeruwa mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajen gaggafar, amma saiwoyinta suka zauna a ƙarƙashinta. Ta haka ta zama kuringa, ta yi rassa ta kuma fid da ganyaye.
And it budded vp, and was like a spreading vine of low stature, whose branches turned toward it, and the rootes thereof were vnder it: so it became a vine, and it brought foorth branches, and shot foorth buds.
7 “‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Kuringan nan ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajen wannan gaggafa daga inda aka shuka ta, ta kuma miƙe rassanta wajenta don gaggafar ta yi mata banruwa.
There was also another great eagle with great wings and many feathers, and beholde, this vine did turne her rootes toward it, and spred foorth her branches toward it, that she might water it by the trenches of her plantation.
8 An shuka ta a ƙasa mai kyau kusa da ruwa mai yawa don tă yi rassa masu yawa, ta ba da’ya’ya ta kuma zama kuringa mai daraja.’
It was planted in a good soyle by great waters, that it should bring forth branches, and beare fruite, and be an excellent vine.
9 “Ka gaya musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa wannan za tă ci gaba? Ba za a tumɓuke ta a kuma kakkaɓe’ya’yanta don ta bushe ba? Dukan sababbin tohonta za su bushe. Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba.
Say thou, Thus saith the Lord God, Shall it prosper? shall he not pull vp the rootes thereof, and destroy the fruite thereof, and cause them to drie? all the leaues of her bud shall wither without great power, or many people, to plucke it vp by the rootes thereof.
10 Ko da an sāke shuka ta, za tă yi amfani ne? Ba za tă bushe gaba ɗaya sa’ad da iskar gabas ta hura ba, tă bushe a ƙasar da ta yi girma?’”
Beholde, it was planted: but shall it prosper? shall it not be dried vp, and wither? when the East winde shall touch it, it shall wither in the trenches, where it grewe.
11 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Moreouer, the worde of the Lord came vnto me, saying,
12 “Ka faɗa wa gidan’yan tawayen nan, ‘Ba ka san abin da waɗannan abubuwa suke nufi ba?’ Ka faɗa musu cewa, ‘Sarkin Babilon ya tafi Urushalima ya tafi da sarkinta da kuma manyan garinta, ya dawo da su Babilon.
Say now to this rebellious house, Know ye not, what these things meane? tell them, Behold, the King of Babel is come to Ierusalem, and hath taken the King thereof, and the princes thereof, and led them with him to Babel,
13 Sa’an nan ya ɗauki wani daga iyalin sarauta ya yi yarjejjeniya da shi, ya sa shi ya yi rantsuwa. Ya kuma tafi da shugabannin ƙasar,
And hath taken one of the Kings seede, and made a couenant with him, and hath taken an othe of him: he hath also taken the princes of the land,
14 don a raunana masarautar, kada tă ƙara tashi, amma ta tsaya dai kan cika yarjejjeniyarsa.
That the kingdome might be in subiection, and not lift it selfe vp, but keepe their couenant, and stand to it.
15 Amma sarkin nan ya yi tawaye a kan sarkin Babilon ta wurin aika jakadunsa zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. Zai ci nasara? Shi da ya yi wannan abu zai tsira? Zai iya taka yarjejjeniya har ya tsere?
But he rebelled against him, and sent his ambassadours into Egypt, that they might giue him horses, and much people: shall hee prosper? shall he escape, that doeth such things? or shall he breake the couenant, and be deliuered?
16 “‘Muddin in raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zai mutu a Babilon, a ƙasar sarkin nan da ya naɗa shi, domin bai cika rantsuwa da alkawarin da ya yi ba.
As I liue, saith the Lord God, he shall die in the middes of Babel, in the place of the King, that had made him King, whose othe he despised, and whose couenant made with him, he brake.
17 Fir’auna da yawan sojojinsa da kuma yawan jama’arsa ba zai zama da taimako gare shi a yaƙi ba, sa’ad da sarkin Babilon zai gina mahaurai ya kuma yi ƙawanya don yă hallaka rayuka masu yawa.
Neither shall Pharaoh with his mightie hoste, and great multitude of people, mainteine him in the warre, when they haue cast vp mounts, and builded ramparts to destroy many persons.
18 Bai cika rantsuwa ba ta wurin take alkawari. Domin sarkin Isra’ila ya ƙulla alkawari ya kuma aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai tsira ba.
For he hath despised the othe, and broken ye couenant (yet lo, he had giuen his hand) because he hath done all these things, he shall not escape.
19 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce muddin ina raye, zan nemi hakkin rantsuwata da ya ƙi cikawa da kuma alkawarin da ya take.
Therefore, thus sayth the Lord God, As I liue, I wil surely bring mine othe that he hath despised, and my couenant that he hath broken vpon his owne head.
20 Zan kafa masa tarkona, zai kuma fāɗi a tarkona. Zan kawo shi a Babilon in kuma hukunta shi a can domin ya yi mini rashin aminci.
And I wil spread my net vpon him, and he shalbe taken in my net, and I wil bring him to Babel, and will enter into iudgement with him there for his trespas that he hath committed against me.
21 Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a kuma watsar da waɗanda suka ragu ko’ina. Ta haka za ku san cewa Ni Ubangiji na faɗa.
And all that flee from him with all his hoste, shall fall by the sword, and they that remaine, shalbe scattered towarde all the windes: and ye shall know that I the Lord haue spoken it.
22 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan cire toho a kan itacen al’ul da yake can bisa in shuka; zan kuma karya ƙanƙanin reshe daga can bisan tohon in shuka a dutse mai tsayi.
Thus saith the Lord God, I wil also take off the top of this hie cedar, and wil set it, and cut off the top of the tender plant thereof, and I wil plant it vpon an hie mountaine and great.
23 A ƙwanƙolin dutsen Isra’ila zan shuka shi; zai yi rassa yă ba da’ya’ya yă kuma zama al’ul mai daraja. Tsuntsaye iri-iri za su yi sheƙa a cikinsa; za su sami mafaka a inuwar rassansa.
Euen in the hie mountaine of Israel will I plant it: and it shall bring forth boughes and beare fruite, and be an excellent cedar, and vnder it shall remaine all birds, and euery foule shall dwell in the shadow of the branches thereof.
24 Dukan itatuwan jeji za su san cewa Ni Ubangiji ne mai sa manyan itatuwa su zama ƙanana in kuma sa ƙananan itatuwa su zama manya. Nakan sa ɗanyen itace ya bushe, busasshen itace kuma ya zama ɗanye. “‘Ni Ubangiji na faɗa, zan kuma aikata.’”
And all the trees of the fielde shall knowe that I the Lord haue brought downe the hie tree, and exalted the lowe tree, that I haue dried vp the greene tree, and made the drie tree to florish: I the Lord haue spoken it, and haue done it.