< Ezekiyel 13 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
And there is a word of YHWH to me, saying,
2 “Ɗan mutum, yi annabci a kan annabawan Isra’ila waɗanda suke annabci yanzu. Ka faɗa wa waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji!
“Son of man, prophesy concerning the prophets of Israel who are prophesying, and you have said to those prophesying from their own heart, Hear a word of YHWH!
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake faɗa, Kaiton wawaye annabawan da suke bin ruhunsu kuma ba su ga kome ba!
Thus said Lord YHWH: Woe to the prophets who are foolish, Who are going after their own spirit, And they have seen nothing.
4 Annabawanki, ya Isra’ila, suna kama da diloli a kufai.
Your prophets have been As foxes in the wasteland, O Israel.
5 Ba ku haura don ku rushe katanga don ku gyara gidan Isra’ila saboda ya tsaya daram a yaƙi a ranar Ubangiji ba.
You have not gone up into breaches, Nor do you make a wall for the house of Israel, To stand in battle in a day of YHWH.
6 Wahayoyinsu ƙarya ne suna yin dubansu na ƙarya ne. Sukan ce, Ubangiji ya furta, alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba; duk da haka sukan sa zuciya ga cikawar maganarsu.
They have seen vanity, and lying divination, Who are saying: A declaration of YHWH, And YHWH has not sent them, And they have hoped to establish a word.
7 Ba ku ga wahayin ƙarya kuka kuma faɗa yin duban ƙarya sa’ad da kuka ce, “Ubangiji ya furta,” ko da yake bai yi magana ba?
Have you not seen a vain vision, And spoken a lying divination, When you say, A declaration of YHWH, And I have not spoken?
8 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa saboda maganganunku na ƙarya da wahayinku na ƙarya, ina gāba da ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Therefore, thus said Lord YHWH: Because you have spoken vanity, and seen a lie, Therefore, behold, I [am] against you, A declaration of Lord YHWH.
9 Hannuna zai yi gāba da annabawan da suke ganin wahayin ƙarya suna kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin gidan Isra’ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
And My hand has been on the prophets, Who are seeing vanity, and who are divining a lie, They are not in the assembly of My people, And they are not written in the writing of the house of Israel, And they do not come to the ground of Israel, And you have known that I [am] Lord YHWH.
10 “‘Domin sun ɓad da mutanena, suna cewa, “Salama,” sa’ad da ba salama, kuma saboda, sa’ad da ana gina katanga marar ƙarfi, sukan shafe ta da farar ƙasa,
Because, even because, they caused My people to err, Saying, Peace! And there is no peace, And that one is building a wall, And behold, they are coating it with chalk.
11 saboda haka ka faɗa wa waɗanda suka shafe da farar ƙasa cewa za tă fāɗi. Ruwan sama zai sauko da rigyawa, zan kuma aika da ƙanƙara, kuma babbar iska za tă ɓarke.
Say to those coating with chalk—It falls, There has been an overflowing shower, And you, O hailstones, fall, And a turbulent wind breaks out,
12 Sa’ad da katangar ta fāɗi, mutane ba za su tambaye ku ba cewa, “Ina shafen farar ƙasar da kuka yi mata?”
And behold, the wall has fallen! Does one not say to you, Where [is] the coating that you coated?
13 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a cikin hasalata zan saki babbar iska, kuma cikin fushina zan tura ƙanƙara kuma rigyawan ruwan sama zai sauko da fushin hallaka.
Therefore, thus said Lord YHWH: I have broken with a turbulent wind in My fury, And an overflowing shower is in My anger, And hailstones in My fury—to consume.
14 Zan rushe katangar da kuka shafe da farar ƙasa zan baje ta har ƙasa saboda tushenta zai tsaya tsirara. Sa’ad da ta fāɗi, za a hallaka ku a cikinta; kuma za ku san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.
And I have broken down the wall that you coated with chalk, And have caused it to come to the earth, And its foundation has been revealed, And it has fallen, And you have been consumed in its midst, And you have known that I [am] YHWH.
15 Ta haka zan aukar wa katangar da hasalata da kuma a kan waɗanda suka yi shafenta da farar ƙasa. Zan ce muku, “Katangar ta fāɗi haka kuma mutanen da suka shafe ta da farar ƙasa,
And I have completed My wrath on the wall, And on those coating it with chalk, And I say to you: The wall is not, And those coating it are not,
16 waɗannan annabawan Isra’ila waɗanda suka yi annabci wa Urushalima suka kuma ga mata wahayin salama sa’ad da ba salama, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”’
[These]—the prophets of Israel, who are prophesying concerning Jerusalem, And who are seeing a vision of peace for her, And there is no peace, A declaration of Lord YHWH.
17 “To, ɗan mutum, ka kafa idonka a kan’yan matan mutanenka waɗanda suke annabci bisa ga ra’ayinsu. Yi annabci a kansu
And you, son of man, set your face against the daughters of your people, who are prophesying out of their own heart, and prophesy concerning them,
18 ka kuma ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton matan da suke ɗinka kambuna a hannuwansu suna kuma yin gyale masu tsawo dabam-dabam wa kawunansu don su farauci mutane. Za ku farauci rayukan mutanena ku bar naku?
And you have said, Thus said Lord YHWH: Woe to those sowing [magic] bands for all joints of the arm, And to those making the veils For the head of every stature—to hunt souls, Do you hunt the souls of My people? And do your souls that live remain alive?
19 Kun jawo mini kunya a cikin mutanena don a tafa muku sha’ir da ɗan dunƙulen burodi. Ta wurin yin ƙarya wa mutanena, waɗanda suke jin ƙarairayi, kuka kashe waɗanda bai kamata su mutu ba kuka bar waɗanda ya kamata su mutu.
Indeed, you pierce Me concerning My people, For handfuls of barley, And for pieces of bread, To put to death souls that should not die, And to keep alive souls that should not live, By your lying to My people—listening to lies.
20 “‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kambunanku waɗanda kuke farautar mutane da su kamar tsuntsaye don haka zan kuma tsintsinke su daga hannuwanku; zan’yantar da mutanen da kuka farauto kamar tsuntsaye.
Therefore, thus said Lord YHWH: Behold, I [am] against your [magic] bands, With which you are hunting there the souls of the flourishing, And I have torn them from off your arms, And have sent away the souls that you are hunting, The souls of the flourishing.
21 Zan kyakketa gyalenku in ceci mutanena daga hannuwanku, ba za su kuma ƙara zama ganima a hannunku ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji
And I have torn your veils, And delivered My people out of your hand, And they are no longer for a prey in your hand, And you have known that I [am] YHWH.
22 Domin kun karya zuciyar masu adalci da ƙarairayinku, sa’ad da na fitar da su babu damuwa, kuma domin kun ƙarfafa mugaye kada su juye daga mugayen hanyoyinsu su ceci rayukansu,
Because of paining the heart of the righteous with falsehood, And I have not pained it, And strengthening the hands of the wicked, So as not to turn [him] back from his evil way, To keep him alive,
23 saboda haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi duba. Zan ceci mutanena daga hannuwanku. A sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.’”
Therefore, you do not see vanity, And you do not divine divination again, And I have delivered My people out of your hand, And you have known that I [am] YHWH!”

< Ezekiyel 13 >