< Ezekiyel 11 >

1 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
Então me levantou o espírito, e me levou à porta oriental da casa do Senhor, que olha para o oriente; e eis que estavam à entrada da porta vinte e cinco homens; e no meio deles vi a Jaazanias, filho de Azus, e a Pelatias, filho de Benaias, príncipes do povo.
2 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
E disse-me: Filho do homem, estes são os homens que pensam na perversidade, e aconselham conselho mau nesta cidade.
3 Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
Que dizem: Não está próximo o tempo de edificar casas; esta cidade é a caldeira, e nós a carne.
4 Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
Portanto, profetiza contra eles: profetiza, ó filho do homem.
5 Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
Caiu pois sobre mim o espírito do Senhor, e disse-me: Dize: Assim diz o Senhor: Assim vós dizeis, ó casa de Israel, porque, quanto às coisas que vos sobem ao espírito, eu as conheço.
6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
Multiplicastes os vossos mortos nesta cidade, e enchestes as suas ruas de mortos.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
Portanto, assim diz o Senhor Jehovah: Vossos mortos, que deitastes no meio dela, esses são a carne, e ela é a caldeira: a vós, porém, vos tirarei do meio dela.
8 Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Temestes a espada, e a espada trarei sobre vós, diz o Senhor Jehovah.
9 Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
E vos farei sair do meio dela, e vos entregarei na mão de estranhos, e exercerei os meus juízos entre vós.
10 Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
Caireis à espada, e nos confins de Israel vos julgarei; e sabereis que eu sou o Senhor.
11 Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
Esta cidade não vos servirá de caldeira, nem vós servireis de carne no meio dela: nos confins de Israel vos julgarei.
12 Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
E sabereis que eu sou o Senhor, porque nos meus estatutos não andastes, nem fizestes os meus juízos; antes fizestes conforme os juízos das nações que estão em redor de vós
13 Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
E aconteceu que, profetizando eu, morreu Pelatias, filho de Benaias: então caí sobre o meu rosto, e clamei com grande voz, e disse: Ah! Senhor Jehovah! porventura farás tu consumação do resto de Israel?
14 Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
Então veio a mim a palavra do Senhor, dizendo:
15 “Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
Filho do homem, teus irmãos, sim, teus irmãos, os homens de teu parentesco, e toda a casa de Israel, todos eles, são aqueles a quem os habitantes de Jerusalém disseram: apartai-vos para longe do Senhor; esta terra se nos deu em possessão.
16 “Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
Portanto, dize: Assim diz o Senhor Jehovah: Ainda que os lancei para longe entre as nações, e ainda que os espalhei pelas terras, todavia lhes servirei de santuário, por um pouco de tempo, nas terras para onde foram.
17 “Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
Portanto, dize: Assim diz o Senhor Jehovah: Ora ajuntar-vos-ei dos povos, e vos recolherei das terras para onde fostes lançados, e vos darei a terra de Israel.
18 “Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
E virão ali, e tirarão dela todas as suas coisas detestáveis e todas as suas abominações.
19 Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
E lhes darei um mesmo coração, e espírito novo porei dentro deles: e tirarei da sua carne o coração de pedra, e lhes darei um coração de carne
20 Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
Para que andem nos meus estatutos, e guardem os meus juízos, e os façam: e eles me serão por povo, e eu lhes serei por Deus.
21 Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Quanto àqueles cujo coração andar conforme o coração das suas coisas detestáveis, e das suas abominações, farei recair nas suas cabeças o seu caminho, diz o Senhor Jehovah
22 Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
Então os cherubins elevaram as suas asas, e as rodas os acompanhavam; e a glória do Deus de Israel estava em cima, sobre eles.
23 Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
E a glória do Senhor se alçou desde o meio da cidade; e se pôs sobre o monte que está defronte do oriente da cidade.
24 Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
Depois o espírito me levantou, e me levou à Chaldea, para os do cativeiro, em visão, pelo espírito de Deus; e subiu de sobre mim a visão que eu tinha visto.
25 na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.
E falei aos do cativeiro todas as coisas que o Senhor me tinha mostrado.

< Ezekiyel 11 >