< Ezekiyel 10 >

1 Na duba, sai na ga kamannin kursiyin saffaya a kan sararin da yake a bisa kawunan kerubobi.
Et je regardai, et voilà que sur le firmament, qui était au-dessus de la tête des chérubins, il y avait comme un saphir, image d'un trône au-dessus d'eux.
2 Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da yake saye da lilin, “Ka shiga cikin da’irorin da suke ƙarƙashin kerubobi. Ka cika hannuwanka da garwashin wuta wanda yake tsakanin kerubobin ka kuma watsar da su a kan birnin.” Yayinda nake dubawa, sai ya shiga.
Et le Seigneur dit à l'homme revêtu d'une longue robe: Entre au milieu des roues sous les chérubins, et prends à pleines mains des charbons au foyer qui est entre les chérubins, et disperse-les sur la ville. Et il y entra devant moi.
3 Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na haikali sa’ad da mutumin ya shiga, sai girgije ya cika filin da yake can ciki.
Et quand l'homme y entra, les chérubins étaient à droite dans le temple, et une nuée remplit le parvis intérieur.
4 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa kerubobi ya tafi zuwa madogarar ƙofar haikali. Girgijen ya cika haikali, filin kuwa ya cika da hasken ɗaukakar Ubangiji.
Alors la gloire du Seigneur s'éleva, et des chérubins passa au portique du temple, et la nuée remplit le temple; et le parvis était rempli des rayons de la gloire du Seigneur.
5 Sai aka ji ƙarar fikafikan kerubobin har a filin waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa’ad da ya yi magana.
Et le bruit des ailes des chérubins s'entendit jusqu'au parvis extérieur, semblable à la voix du Dieu tout-puissant quand il parle.
6 Sa’ad da Ubangiji ya umarci mutumin da yake saye da lilin cewa, “Ka ɗibi wuta daga cikin tsakanin da’irorin, daga tsakanin kerubobin,” sai mutumin ya shiga ya tsaya kusa da da’irar.
Et ceci advint: pendant que le Seigneur donnait ses ordres à l'homme revêtu de la robe sainte, disant: Prends du feu au milieu des roues, parmi les chérubins; l'homme entra et s'arrêta près des roues.
7 Sa’an nan ɗaya daga cikin kerubobin ya miƙa hannu zuwa wurin wutar da take tsakaninsu. Ya ɗebo wutar daga ciki ya zuba a hannuwan mutumin da yake saye da lilin, shi kuwa ya karɓa ya fita.
Et le Seigneur étendit la main sur le feu qui était parmi les chérubins, et il en prit, et il en remplit les mains de l'homme qui était revêtu de la robe sainte; et celui-ci le prit, et il sortit.
8 (A ƙarƙashin fikafikan kerubobin ana iya ganin abin da ya yi kamar hannuwan mutum.)
Et je vis les chérubins ayant l'image d'une main d'homme sur leurs ailes.
9 Na duba, sai na ga kusa da kerubobin akwai da’irori huɗu, kowanne kusa da kerub guda; da’irorin suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja.
Et je vis, et voilà que les quatre roues étaient arrêtées près des chérubins; chaque roue touchait un chérubin, et l'aspect des roues était comme l'aspect d'une escarboucle.
10 Game da kamanninsu kuwa, huɗu a cikinsu sun yi kama da juna; kowanne ya yi kamar da da’ira a cikin da’ira.
Et, quant à leur aspect; elles avaient toutes les quatre le même aspect, c'était comme si une roue était au milieu d'une roue.
11 Yayinda suke tafiya, sukan tafi kowane gefe huɗun da kerubobin suka nufa; da’irorin ba sa juyawa yayinda kerubobin suke tafiya. Kerubobin suka tafi kowane gefen da kan ya nufa, ba tare da juyawa ba sa’ad da suke tafiya.
Lorsqu'elles allaient, elles allaient de leurs quatre parties, et en allant elles ne se retournaient pas; quel que fut le lieu qu'avait regardé la première tète, elles y allaient, et, en allant, elles ne se retournaient pas.
12 Jikunansu gaba ɗaya, har da bayansu, hannuwansu da fikafikansu, sun cika gaba ɗaya da idanu, kamar yadda suke a da’irori huɗun.
Et leurs moyeux, leurs mains, leurs ailes et leurs bandes étaient pleins d'yeux, tout alentour aux quatre roues.
13 Na ji ana kiran da’irorin “da’irorin guguwa.”
Et tandis que j'écoutais, le nom de Gelgel fut donné aux quatre roues.
14 Kowane daga kerubobin yana da fuskoki huɗu. Fuska ɗaya na kerub ne, na biyun fuskar mutum ne, na ukun fuskar zaki ne, na huɗun kuwa fuskar gaggafa ce.
15 Sai kerubobin suka tashi sama. Waɗannan ne halittu masu ran da na gani kusa da Kogin Kebar.
Et les chérubins étaient ces mêmes créatures vivantes que j'avais vues sur le fleuve Chobar.
16 Sa’ad da kerubobin suka motsa, sai da’irorin da suke kusa da su su motsa; kuma sa’ad da kerubobin suka buɗe fikafikansu don su tashi daga ƙasa, da’irorin ba sa barin wurarensu.
Et quand les chérubins allaient, les roues allaient, et elles étaient tout près d'eux; et quand les chérubins étendaient les ailes pour s'élever au- dessus de terre, les roues ne se détournaient point d'eux.
17 Sa’ad da kerubobin suka tsaya cik, su ma sukan tsaya cik; kuma sa’ad da kerubobin suka tashi, sai su ma su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun yana a cikinsu.
Et quand ils s'arrêtaient, elles s'arrêtaient; et quand ils s'élevaient, elles s'élevaient avec eux, parce qu'il y avait en elles un esprit de vie.
18 Sai ɗaukakar Ubangiji ya tashi daga bisa madogarar ƙofar haikali ya kuma tsaya a bisa kerubobi.
Et la gloire du Seigneur sortit du temple, et alla sur les chérubins.
19 Yayinda nake duba, kerubobin suka buɗe fikafikansu suka kuma tashi daga ƙasa, yayinda suka tafi kuwa, da’irorin suka tafi tare da su. Suka tsaya a mashigin ƙofar gabas na gidan Ubangiji, ɗaukakar Allah na Isra’ila kuwa yana a kansu.
Et les chérubins déployèrent leurs ailes, et ils planèrent au-dessus de terre devant moi; lorsqu'ils partirent, les roues étaient toujours auprès d'eux, et ils s'arrêtèrent sur le vestibule de la façade du temple du Seigneur; et la gloire du Dieu d'Israël était sur eux.
20 Waɗannan ne rayayyun halittun da na gani a ƙarƙashin Allah na Isra’ila kusa da Kogin Kebar, na kuma gane cewa su kerubobi ne.
Et c'étaient les créatures vivantes que j'avais vues au-dessous du Dieu d'Israël, vers le fleuve de Chobar, et je reconnus que c'étaient des chérubins.
21 Kowanne yana da fuskoki huɗu da fikafikai huɗu, a ƙarƙashin kuwa akwai wani abin da ya yi kamar hannuwan mutum.
Chacun avait quatre faces et huit ailes, et sous les ailes l'image d'une main d'homme.
22 Fuskokinsu suna da kamanni ɗaya da waɗanda na gani kusa da Kogin Kebar. Kowanne ya tafi kai tsaye sosai.
Et leurs visages se ressemblaient, et c'étaient les visages que j'avais vus sous la gloire du Dieu d'Israël, vers le fleuve Chobar, et chacun marchait droit devant lui.

< Ezekiyel 10 >