< Fitowa 7 >

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
Then Yahweh said to Moses/me, “Listen [carefully]. [Just like I enabled prophet to speak my messages], I will cause the king [to consider that] you are like a god, and that Aaron is like a prophet.
2 Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
You must tell everything I command you [to tell to your older] brother Aaron, and he will tell that to the king. He must tell the king to let the Israeli people leave his land.
3 Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
But I will make the king stubborn [IDM]. As a result, even though I perform many kinds of (miracles/terrifying things) [DOU] [here] in Egypt,
4 ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
the king will not pay any attention to what you say. Then I will punish [MTY] the people of Egypt [MTY] very severely [MTY], and I will lead/bring the tribes of the Israeli people out of Egypt.
5 Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
Then, when I show my great power [MTY] to the Egyptian people and bring the Israeli people out from among them, they will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do].”
6 Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
Aaron and Moses/I did what Yahweh told them/us to do. They/We [went and spoke to the king].
7 Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
At that time, Moses/I was 80 years old, and Aaron was 83 years old.
8 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
Yahweh said to Moses/me,
9 “Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
“If the king says to you, ‘Prove [that God sent] you by performing a miracle,’ then say to Aaron, ‘Throw your stick down in front of the king, in order that it may become a snake.’”
10 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
So Aaron and Moses/I went to the king and did what Yahweh had commanded [them/us to do]. Aaron threw his stick down in front of the king and his officials, and it became a snake.
11 Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
Then the king summoned his sorcerers and men who performed magic. They did the same thing, using their magic.
12 Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
They all threw down their sticks, and they became snakes. But Aaron’s stick, [which had become a snake], swallowed up all their sticks!
13 Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
But the king continued to be stubborn [IDM], just as Yahweh had predicted, and he would not pay attention to [what Aaron and Moses/I said].
14 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
Then Yahweh said to Moses/me, “The king is very stubborn [IDM]. He refuses to allow [my] people to go.
15 Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
So [tomorrow] morning, go to him as he is going down to the [Nile] River [to bathe]. Wait for him at the riverbank. [When he comes out of the water, show] him the stick, the one which became a snake.
16 Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
Say to him, ‘Yahweh God, the one [we] Hebrews [worship], sent me to you to tell you to let my people go, in order that they may worship him in the desert. [We told you that], but you have not paid any attention to it.
17 Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
[So now] Yahweh says this: “This is the way you will know that I, Yahweh, [have the power to do what I say that I will do]. Watch this: I am going to strike the water that is in the Nile [River] with the stick that is in my hand. [When I do that], the water will become blood (OR, [red like] blood [MTY]).
18 Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
Then the fish in the Nile [River] will die, and the [water in] the river will stink, and the Egyptians will not be able to drink water from the Nile River.”’”
19 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
Yahweh said to Moses/me, “[When you are talking to the king], say to Aaron, ‘Hold your stick out [as though you were holding it] over the water in Egypt—over the rivers, the canals, the ponds, and over the pools of water, in order that [all of it] may become [red like] blood.’ When Aaron does that, there will be blood throughout Egypt, even in wooden jars and in stone jars.”
20 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
So Aaron and Moses/I did what Yahweh commanded. As the king and his officials were watching, Aaron lifted up his stick and then struck the water in the Nile [River] with it. And all the water in the river turned [red like] blood.
21 Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
Then all the fish died. And the water stank, with the result that the Egyptians could not drink water from the river. Everywhere in Egypt [the water] became [red like] blood.
22 Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
But the men who performed magic did the same thing using their magic. So the king remained stubborn [IDM], and he would not pay attention to what Aaron and Moses/I said, just as Yahweh had predicted.
23 A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
The king turned and went back to his palace, and he did not think any more about it [IDM].
24 Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
The Egyptians [HYP] dug [into the ground] near the Nile [River] to get water to drink, because they could not drink the water from the river.
25 Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.
(One week/Seven days) passed after Yahweh caused the water in the Nile [River to become red like blood].

< Fitowa 7 >