< Fitowa 33 >
1 Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka bar wannan wuri, kai da mutanen da ka fito da su daga Masar, ka haura zuwa ƙasar da na alkawarta da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub cewa, ‘Zan ba zuriyarka.’
And Jehovah spoke to Moses, Depart, go up from here, thou and the people that thou have brought up out of the land of Egypt, to the land of which I swore to Abraham, to Isaac, and to Jacob, saying, To thy seed will I give it.
2 Zan aika da mala’ika a gabanka in kuma kori Kan’aniyawa, Amoriyawa, Hittiyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa.
And I will send an agent before thee, and I will drive out the Canaanite, the Amorite, and the Hittite, and the Perizzite, the Hivite, and the Jebusite-
3 Ka haura zuwa ƙasar da take zub da madara da zuma. Amma ba zan tafi tare da ku ba, saboda ku mutane ne masu taurinkai domin mai yiwuwa in hallaka ku a hanya.”
to a land flowing with milk and honey. For I will not go up in the midst of thee, for thou are a stiff-necked people, lest I consume thee on the way.
4 Da mutane suka ji wannan mugun magana, sai suka fara makoki. Ba kuma wanda ya sa kayan ado.
And when the people heard these evil tidings, they mourned, and no man put his ornaments on him.
5 Gama Ubangiji ya riga ya ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurinkai. In na yi tafiya da ku ko na ɗan lokaci, mai yiwuwa in hallaka ku. Yanzu sai ku tuɓe kayan adonku, zan kuwa yanke shawara a kan abin da zan yi da ku.’”
And Jehovah said to Moses, Say to the sons of Israel, Ye are a stiff-necked people. If I go up into the midst of thee for one moment, I shall consume thee. Therefore now put off thy ornaments from thee, that I may know what to do to thee.
6 Saboda haka Isra’ilawa suka tuttuɓe kayan adonsu a Dutsen Horeb.
And the sons of Israel stripped themselves of their ornaments from mount Horeb onward.
7 Musa fa ya saba ɗaukan tenti yă kafa shi a bayan sansani da ɗan nisa, yana kiransa “Tentin Sujada.” Duk wanda yake neman wani abu daga wurin Ubangiji sai yă tafi Tentin Sujada a bayan sansani.
Now Moses used to take the tent and to pitch it outside the camp, afar off from the camp, and he called it, The tent of meeting. And it came to pass, that everyone who sought Jehovah went out to the tent of meeting, which was outside the camp.
8 A sa’ad da kuma Musa ya fita zuwa Tentin, dukan mutanen sukan tashi su tsaya a ƙofofin tentinsu, suna kallon Musa, sai ya shiga tentin.
And it came to pass, when Moses went out to the tent, that all the people rose up, and stood, every man at his tent door, and looked after Moses, until he was gone into the tent.
9 Yayinda Musa ya shiga cikin tentin, sai al’amudin girgije yă sauko, yă tsaya a ƙofar yayinda Ubangiji yana magana da Musa.
And it came to pass, when Moses entered into the tent, the pillar of cloud descended, and stood at the door of the tent, and Jehovah spoke with Moses.
10 Lokacin da mutane suka ga al’amudin girgije a tsaye a ƙofar tentin, sai duk su miƙe tsaye su yi sujada, kowa a ƙofar tentinsa.
And all the people saw the pillar of cloud stand at the door of the tent. And all the people rose up and worshiped, every man at his tent door.
11 Ubangiji yakan yi magana da Musa fuska da fuska, kamar yadda mutum yake magana da abokinsa. Sa’an nan Musa yă koma sansani, amma saurayin nan Yoshuwa ɗan Nun mai taimakonsa ba ya barin tentin.
And Jehovah spoke to Moses face to face, as a man speaks to his friend, and he turned again into the camp. But his minister Joshua, the son of Nun, a young man, did not depart out of the tent.
12 Musa ya ce wa Ubangiji, “Kana ta faɗa mini cewa, ‘Ka jagoranci mutane nan,’ amma ba ka faɗa mini wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi ka ƙara ce mini, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a wurina.’
And Moses said to Jehovah, See, thou say to me, Bring up this people, and thou have not let me know whom thou will send with me. Yet thou have said, I know thee by name, and thou have also found favor in my sight.
13 In ka ji daɗina, ka koya mini hanyarka don in san ka, in kuma ci gaba da samun tagomashi daga gare ka. Ka tuna cewa wannan al’umma mutanenka ne.”
Now therefore, I pray thee, if I have found favor in thy sight, show me now thy ways, that I may know thee, to the end that I may find favor in thy sight. And consider that this nation is thy people.
14 Ubangiji ya amsa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma rage maka nauyin kaya.”
And he said, My presence shall go with thee, and I will give thee rest.
15 Musa kuwa ya ce masa, “In ba za tă tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan.
And Moses said to him, If thy presence go not, do not carry us up from here.
16 Yaya wani zai sani ko ka ji daɗina da kuma mutanenka, in ba ka tafi tare da mu ba? Mene ne kuma zai bambanta ni da mutanenka daga sauran jama’ar da suke a duniya?”
For how shall it now be known that I have found favor in thy sight, I and thy people? Is it not in that thou go with us, so that we are separated, I and thy people, from all the people that are upon the face of the earth?
17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka faɗa, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.”
And Jehovah said to Moses, I will do this thing also that thou have spoken, for thou have found favor in my sight, and I know thee by name.
18 Musa kuwa ya ce, “To, ka nuna mini ɗaukakarka.”
And he said, Show me, I pray thee, thy glory.
19 Sai Ubangiji ya ce, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka. Zan yi alheri ga duk wanda na so in yi masa alheri, zan nuna jinƙai ga duk wanda na so in yi masa jinƙai.
And he said, I will make all my goodness pass before thee, and will proclaim the name of Jehovah before thee. I will be merciful to whom I may be merciful, and I will be compassionate to whomever I may be compassionate.
20 Amma ya ce, ba za ka ga fuskata ba, don ba mutumin da zai gan ni yă rayu.”
And he said, Thou cannot see my face, for man shall not see me and live.
21 Sa’an nan Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen.
And Jehovah said, Behold, there is a place by me, and thou shall stand upon the rock.
22 A sa’ad da ɗaukakata tana wucewa, zan sa ka a cikin tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har sai na wuce.
And it shall come to pass, while my glory passes by, that I will put thee in a cleft of the rock, and will cover thee with my hand until I have passed by.
23 Sa’an nan zan ɗauke hannuna, ka kuwa ga bayana; amma fuskata, ba za ka gani ba.”
And I will take away my hand, and thou shall see my back, but my face shall not be seen.