< Fitowa 3 >

1 Ana nan wata rana Musa yana kiwon tumakin Yetro surukinsa, firist na Midiyan, sai ya bi da tumaki zuwa gefe mai nisa a cikin hamada, har ya zo Horeb, dutsen Allah.
Torej Mojzes je varoval trop svojega tasta Jitra, midjánskega duhovnika in vodil trop k zadnjemu delu puščave in prišel h gori Boga, k Horebu.
2 A can mala’ikan Ubangiji ya bayyana a gare shi cikin harshen wuta, a ƙaramin itace. Musa ya lura cewa ko da yake wuta na ci ƙaramin itacen, amma bai ƙone ba.
Gospodov angel se mu je prikazal v ognjenem plamenu iz srede grma in pogledal je in glej, grm je gorel z ognjem, pa grm ni bil použit.
3 Sai Musa ya ce, “Wannan abin mamaki ne, don me wannan itace bai ƙone ba? Bari in matso kusa in gani.”
Mojzes je rekel: »Sedaj se bom obrnil vstran in pogledal ta velik prizor, zakaj grm ne zgori.«
4 Da Ubangiji ya ga Musa ya matso don yă duba, sai Allah ya yi kira daga cikin ƙaramin itacen ya ce, “Musa! Musa!” Sai Musa ya amsa ya ce, “Ga ni.”
Ko je Gospod videl, da se je obrnil vstran, da bi videl, je Bog iz srede grma zaklical k njemu ter rekel: »Mojzes, Mojzes.« Ta je rekel: »Tukaj sem.«
5 Allah ya ce, “Kada ka zo kusa, tuɓe takalmanka, gama inda kake tsaye, wuri ne mai tsarki.”
Rekel je: »Ne približaj se, svoje čevlje sezuj s svojih stopal, kajti prostor, na katerem stojiš, je sveta zemlja.«
6 Sai Allah ya ce, “Ni ne Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub.” Da jin wannan, sai Musa ya ɓoye fuskarsa, domin ya ji tsoro yă dubi Allah.
Poleg tega je rekel: »Jaz sem Bog tvojega očeta, Bog Abrahama, Bog Izaka in Bog Jakoba.« In Mojzes je skril svoj obraz, kajti bal se je, da bi pogledal na Boga.
7 Ubangiji ya ce, “Tabbatacce na ga azabar mutanena a Masar. Na ji su suna kuka saboda matsin da shugabannin gandunsu suke musu, na kuma damu da wahalarsu.
Gospod je rekel: »Zagotovo sem videl stisko svojega ljudstva, ki je v Egiptu in slišal njihovo vpitje zaradi njihovih preddelavcev, kajti poznam njihove bridkosti
8 Saboda haka na sauko domin in cece su daga hannun Masarawa, in kuma fitar da su daga ƙasar Masar, in kai su ƙasa mai kyau mai fāɗi, ƙasa mai zub da madara da zuma, inda Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa suke.
in prišel sem dol, da jih osvobodim iz roke Egipčanov in jih privedem iz te dežele gor v dobro in veliko deželo, deželo, kjer tečeta mleko in med, v deželo Kánaancev, Hetejcev, Amoréjcev, Perizéjcev, Hivéjcev in Jebusejcev.
9 Yanzu kukan Isra’ilawa ya kai gare ni, na kuma ga yadda Masarawa suke wulaƙanta su
Zdaj torej, glej, k meni je prišlo vpitje Izraelovih otrok in videl sem tudi zatiranje, s kakršnim so jih Egipčani zatirali.
10 To, fa, sai ka tafi. Ina aikan ka wurin Fir’auna don ka fitar da mutanena Isra’ilawa daga Masar.”
Pridi torej zdaj in jaz te bom poslal k faraonu, da lahko privedeš moje ljudstvo, Izraelove otroke, iz Egipta.«
11 Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi wurin Fir’auna, in kuma fitar da Isra’ilawa daga Masar?”
Mojzes pa je Bogu rekel: »Kdo sem jaz, da bi šel k faraonu in da bi lahko Izraelove otroke privedel iz Egipta?«
12 Sai Allah ya ce, “Zan kasance da tare kai. Wannan kuwa za tă zama alama a gare ka cewa Ni na aike ka. Bayan ka fitar da mutanen daga Masar, za ku yi sujada ga Allah a kan dutsen nan.”
Rekel je: »Zagotovo bom s teboj in to ti bodi simbol, da sem te jaz poslal. Ko boš ljudstvo privedel iz Egipta, boste na tej gori služili Bogu.«
13 Musa ya ce wa Allah, “A ce ma na tafi wurin Isra’ilawa na ce musu, ‘Allah na kakanninku ya aiko ni wurinku,’ in suka tambaye ni, ‘Mene ne sunansa?’ Me zan ce?”
Mojzes je Bogu rekel: »Glej, ko pridem k Izraelovim otrokom in jim bom rekel: ›K vam me je poslal Bog vaših očetov, ‹ pa mi bodo rekli: ›Kakšno je njegovo ime?‹ Kaj naj jim rečem?«
14 Allah ya ce wa Musa, “NI NE wanda NINE. Abin da za ka faɗa wa Isra’ilawa ke nan cewa, ‘NI NE, ya aiko ni wurinku.’”
Bog je Mojzesu rekel: »JAZ SEM, KI SEM.« Rekel je: »Tako boš govoril Izraelovim otrokom: ›JAZ SEM me je poslal k vam.‹«
15 Allah ya kuma ce wa Musa, “Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Ubangiji, Allah na kakanninka, Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub, ya aiko ni wurinku.’ Wannan shi ne sunana har abada, sunan da za a tuna da ni daga tsara zuwa tsara ke nan.
Bog je Mojzesu poleg tega povedal: »Tako boš rekel Izraelovim otrokom: ›K vam me je poslal Gospod, Bog vaših očetov, Bog Abrahama, Bog Izaka in Bog Jakoba. To je moje ime na veke in to je moj spomin vsem rodovom.‹
16 “Tafi ka tattara dattawan Isra’ila, ka ce musu, ‘Ubangiji, Allah na kakanninku, Allah na Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, ya bayyana a gare ni ya ce, Na lura da ku, na kuma ga abubuwan da ake yi muku a Masar.
Pojdi in zberi skupaj vse Izraelove starešine ter jim reci: ›Prikazal se mi je Gospod, Bog vaših očetov, Bog Abrahama, Izaka in Jakoba, rekoč: ›Zagotovo sem vas obiskal in videl to, kar vam je storjeno v Egiptu.‹«
17 Na kuma yi alkawari, zan fitar da ku daga azabarku a Masar zuwa ƙasar Kan’aniyawa, Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, ƙasa mai zub da madara da zuma.’
In rekel sem: »Jaz vas bom privedel gor iz egiptovske stiske v deželo Kánaancev, Hetejcev, Amoréjcev, Perizéjcev, Hivéjcev in Jebusejcev, v deželo, kjer tečeta mleko in med.
18 “Dattawan Isra’ila za su saurare ka. Sa’an nan da kai da dattawan Isra’ila, za ku tafi wurin sarkin Masar, ku ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya sadu da mu. Bari mu yi tafiyar kwana uku zuwa cikin hamada domin mu yi hadaya wa Ubangiji Allahnmu.’
Prisluhnili bodo tvojemu glasu in ti boš prišel, ti in Izraelove starešine, k egiptovskemu kralju in mu boste rekli: › Gospod, Bog Hebrejcev, se je srečal z nami in sedaj nas pusti iti, rotimo te, tri dni potovanja v divjino, da bomo lahko žrtvovali Gospodu, našemu Bogu.‹
19 Amma na san cewa sarkin Masar ba zai yarda ku tafi ba, sai hannu mai ƙarfi ya tilasta shi.
Prepričan pa sem, da vam egiptovski kralj ne bo pustil oditi, ne, niti z mogočno roko ne.
20 Saboda haka zan miƙa hannuna in bugi Masarawa da duk al’ajaban da zan aikata a cikinsu. Bayan haka zai bar ku, ku tafi.
Svojo roko bom iztegnil in Egipt udaril z vsemi čudeži, ki jih bom storil v njihovi sredi in nató vas bo pustil oditi.
21 “Zan kuma sa mutanen su sami tagomashi daga wurin Masarawa, saboda sa’ad da za ku fita, ba za ku fita hannu wofi ba.
Temu ljudstvu bom dal naklonjenost v očeh Egipčanov in zgodilo se bo, ko greste, da ne boste odšli prazni,
22 Kowace mace ta tambayi maƙwabciyarta, da kuma duk wata macen da take cikin gidanta, kayayyakin azurfa da na zinariya da kuma na riguna, waɗanda za ku sa wa’ya’yanku maza da mata. Ta haka nan za ku washe Masarawa.”
temveč si bo vsaka ženska izposodila od sosede in od tiste, ki začasno biva v njeni hiši, dragocenosti iz srebra in dragocenosti iz zlata in oblačil, in vi jih boste nadeli na svoje sinove in na svoje hčere in boste oplenili Egipčane.«

< Fitowa 3 >