< Fitowa 21 >

1 “Waɗannan su ne dokokin da za ka sa a gabansu.
“Here are some [other] instructions to give to [the Israeli people]:
2 “In ka sayi mutumin Ibraniyawa a matsayin bawa, zai bauta maka shekara shida. Amma a shekara ta bakwai, za ka’yantar da shi, yă tafi’yantacce, ba tare da ya biya kome ba.
When/If you buy a Hebrew slave, he is to serve you for [only] six years. In the seventh year you must free him [from being your slave], and he is not required to pay you anything [for setting him free].
3 In ya zo shi kaɗai, zai tafi’yantacce shi kaɗai; amma in yana da mata a lokacin da ya zo, za tă tafi tare da shi.
If he was not married before he became your slave, and if he marries [someone while he is your slave], his wife is not to be set free [with him]. But if he was married before he became your slave, you must free both him and his wife.
4 In maigidansa ya yi masa aure, ta kuwa haifa masa’ya’ya maza ko mata, matan da’ya’yan, za su zama na maigidan, sai mutumin kaɗai zai tafi’yantacce.
If a slave’s master gives him a wife, and she gives birth to sons or daughters [while her husband is a slave], only the man is to be freed. His wife and children will continue to be slaves of their master.
5 “Amma in bawan ya furta ya ce, ‘Ina ƙaunar maigidana, da matata, da’ya’yana, ba na so kuma in’yantu,’
But when it is time for the slave to be set free, if the slave says, ‘I love my master and my wife and my children, and I do not want to be set free,’
6 dole maigidansa yă kai shi gaban alƙalai. Zai kai shi ƙofa ko madogarar ƙofa, yă huda kunnensa da basilla, sa’an nan zai zama bawansa duk tsawon kwanakinsa a duniya.
then his master must take him to [the place where they worship] God (OR, to [the owner’s] house). There he must make the slave stand against the door or the doorpost. Then the master will use an (awl/pointed metal rod) to make a hole in the slave’s ear. Then [he will fasten a tag to the slave’s ear to indicate that] (he will own that slave for the rest of his life/he will own the slave as long as the slave lives).
7 “In mutum ya sayar da’yarsa a matsayin baiwa, ba za a’yantar da ita kamar bawa ba.
If a man sells his daughter to become a slave, she should not be set free [after six years], as the male slaves are.
8 In ba tă gamshi maigida wanda ya zaɓe ta domin kansa ba, dole yă bari a fanshe ta. Ba shi da dama yă sayar da ita ga baƙi, tun da yake bai kyauta mata ba.
If the man who bought her wanted her to be his wife, but if [later] he is not pleased with her, he must sell her back to her father. He must not sell her to a foreigner, because that would be breaking the contract/agreement [he made with the girl’s father].
9 In ya zaɓe ta domin ɗansa, dole yă ba ta duk damar da’ya ta mace take da shi.
If the man who buys her wants her to be a wife for his son, he must then treat her as though she were his own daughter.
10 In ya auri wata mace, ba zai hana wa baiwar abinci da sutura ba, ba kuma zai ƙi kwana da ita ba.
If the master takes another slave girl to be another wife for himself, he must continue to give the first slave wife the same amount of food and clothing that he gave to her before, and he must continue to have sex [EUP] with her as before.
11 In bai tanada mata waɗannan abubuwa uku ba, sai tă tafi’yantacciya, babu biyan kome.
If he does not do all these three things for her, he must free her [from being a slave], and she is not required to pay anything [for being set free].
12 “Duk wanda ya bugi mutum har ya kashe shi, lalle a kashe shi.
You must execute anyone who strikes another person with the result that the person who is struck dies.
13 Amma in ba da nufin yă kashe shi ba, sai dai in Allah ne ya nufa haka, to, sai mutumin yă tsere zuwa inda zan nuna muku.
But if the one who struck the other did not intend to kill that person, the one who struck him can escape to a place that I will choose for you, [and he will be safe there].
14 Amma in mutumin ya yi dabara har ya kashe wani mutum da gangan, sai a ɗauke shi daga bagadena a kashe shi.
But if someone gets angry with another person and kills him, even if the murderer runs to the altar, [a place that God designated as a place to be safe], you must execute him.
15 “Duk wanda ya bugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
Anyone who strikes his father or mother must surely be executed.
16 “Duk wanda ya saci mutum ya sayar da shi, ko kuwa aka iske shi a hannunsa, lalle kashe shi za a yi.
Anyone who kidnaps another person, either in order to sell that person or to keep him as a slave, must be executed.
17 “Duk wanda ya la’anta mahaifinsa ko mahaifiyarsa, dole a kashe shi.
Anyone who reviles/curses his father or his mother must be executed.
18 “Idan mutane suka yi faɗa, ɗayan ya jefa ɗayan da dutse, ko ya naushe shi amma bai mutu ba, sai dai ya yi ta jiyya,
Suppose two people fight, and one strikes the other with a stone or with his fist. And suppose the person he strikes does not die but is injured and has to stay in bed [for a while],
19 idan mutumin ya sāke tashi ya yi tafiya ko da yana dogarawa da sanda ne, wanda ya buge shi zai kuɓuta, sai dai zai biya diyyar lokacin da ya ɓata masa, yă kuma lura da shi, har yă warke sarai.
and later he is able to walk outside using a cane. Then the person who struck him does not have to be punished. However, he must pay the injured person the money he could not earn [while he was recovering], and he must also pay the injured person’s medical expenses until that person is well.
20 “In mutum ya dūke bawansa ko baiwarsa da sanda, sai bawan ko baiwar ta mutu saboda dūkan, dole a hukunta shi,
If someone strikes his male or female slave with a stick, if the slave dies (immediately/as a result) [IDM], the one who struck him must be punished.
21 amma ba za a hukunta shi ba, in bawan ko baiwar ta tashi, bayan kwana ɗaya ko biyu, tun da bawan ko baiwar mallakarsa ne.
But if the slave lives for a day or two after he is struck [and then dies], you must not punish the one who struck him. Not having that slave to be able to work for him any longer is enough punishment.
22 “Idan mutum biyu suna faɗa, har suka yi wa mace mai ciki rauni, har ya sa ta yi ɓari, amma wani lahani bai same ta ba, za a ci wa wanda ya yi mata raunin tara bisa ga yadda mijinta ya yanka za a biya, in dai abin da ya yanka ya yi daidai da abin da alƙalai suka tsara.
Suppose two people are fighting and they hurt a pregnant woman with the result that (she has a miscarriage/her baby is born prematurely and dies). If the woman is not harmed in any other way, the one who injured her must pay a fine. He must pay whatever the woman’s husband demands, after a judge approves of the fine.
23 Amma in akwai rauni mai tsanani, sai a ɗauki rai a maimakon rai,
But if the woman is injured in some additional way, the one who injured her must be caused to suffer in exactly the same way [that he caused her to suffer]. If she dies, he must be executed.
24 ido don ido, haƙori don haƙori, hannu don hannu, ƙafa don ƙafa,
If her eye is injured or destroyed, or if he knocks out one of her teeth, or her hand or foot is injured, or if she is burned or bruised, the one who injured her must be injured in the same way.
25 ƙuna don ƙuna, rauni don rauni, ƙujewa don ƙujewa.
26 “In mutum ya bugi bawa ko baiwa a ido, har idon ya lalace, dole yă’yantar da shi ko ita, maimakon ido.
If the owner of a slave strikes the eye of his male or female slave and ruins it, he must free that slave because of [what he did to] the slave’s eye.
27 In kuma ya fangare haƙorin bawa ko baiwa, dole yă’yantar da bawan ko baiwar, a maimakon haƙorin.
If someone knocks out one of his slave’s teeth, he must free the slave because of [what he did to] the slave’s tooth.
28 “In bijimi ya kashe namiji ko ta mace, dole a jajjefe bijimin har yă mutu, ba za a kuma ci namansa ba. Amma mai bijimin ba shi da laifi.
If a bull gores a man or woman with the result that the person dies, you [must kill the bull by] throwing stones at it, but you must not punish the owner of the bull.
29 In, har an san bijimin da wannan hali, an kuma yi wa mai shi gargaɗi, amma bai ɗaura shi ba, har ya kashe namiji ko ta mace, za a jajjefe bijimin tare da mai shi, har su mutu.
But suppose the bull had attacked people several times before, and its owner had been warned, but he did not keep the bull inside a fence. Then you [must kill the bull by] throwing stones at it, but you must also execute its owner.
30 Amma fa, in an bukace shi yă biya, zai biya don yă fanshi ransa ta wurin biyan abin da aka aza masa.
However, if the owner of the bull is allowed to pay a fine (to save his own life/in order not to be executed), he must pay the full amount that the judges say that he must pay.
31 Wannan doka ta shafi batun bijimin da ya kashe ɗa ko’ya.
If someone’s bull attacks and gores another person’s son or daughter, you must treat the bull’s owner according to that same rule.
32 In bijimin ya kashe bawa ko baiwa, mai shi zai biya shekel talatin na azurfa wa maigidan bawan, a kuma a jajjefe bijimin.
If a bull attacks and gores a male or female slave, its owner must pay to the slave’s owner 30 pieces of silver. Then you must [kill the bull by] throwing stones at it.
33 “In mutum ya bar rami a buɗe, ko ya haƙa rami bai kuma rufe ba, sai saniya ko jaki ya fāɗi a ciki,
Suppose someone has a pit/cistern and does not keep it covered, and someone’s bull or donkey falls into it [and dies].
34 Mai ramin zai biya rashin da aka yi wa mai shi, matacciyar saniyan ko jakin, zai zama na mai ramin.
Then the owner of the pit/cistern must pay for the animal that died. He must give the money to the animal’s owner, but then he can take away the animal that died and [do whatever he wants to with it].
35 “In bijimin mutum ya raunana bijimin wani, har ya mutu, sai mutanen biyu su sayar da mai ran, su raba kuɗin daidai, haka ma su yi da mai ran.
If someone’s bull hurts another person’s bull with the result that it dies, the owners of both bulls must sell the bull that is living, and they must divide [between them] the money [that they receive] for it. They must also divide [between them the meat of] the animal that died.
36 Amma fa, in tun can, an san bijimin yana da wannan halin faɗa, duk da haka mai shi bai ɗaura shi ba, dole mai shi yă biya, dabba domin dabba, matacciyar dabbar kuwa tă zama nasa.
However, if people know that the bull often attacked other animals previously, and its owner did not keep it inside a fence, then the owner of that bull must give the owner of the bull that died one of his own bulls, but he can take away the animal that died [and do with it whatever he wants to do].”

< Fitowa 21 >