< Fitowa 16 >

1 Dukan taron Isra’ila suka tashi daga Elim suka zo hamadar Sin, wadda take tsakanin Elim da Sinai, a rana ta goma sha biyar ga wata biyu, bayan sun fito daga Masar.
And they journey from Elim, and all the congregation of the sons of Israel come to the wilderness of Sin, which [is] between Elim and Sinai, on the fifteenth day of the second month of their going out from the land of Egypt.
2 A hamadan, dukan taro suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna.
And all the congregation of the sons of Israel murmur against Moses and against Aaron in the wilderness;
3 Isra’ilawa suka ce musu, “Da ma a hannun Ubangiji ne muka mutu a Masar, inda muka zauna kewaye da tukwanen nama, muna cin duk abincin da muke so, amma kun kawo mu cikin wannan hamada don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.”
and the sons of Israel say to them, “Oh that we had died by the hand of YHWH in the land of Egypt, in our sitting by the flesh-pot, in our eating bread to satiety—for you have brought us out to this wilderness to put all this assembly to death with hunger.”
4 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan zubo muku burodi kamar ruwa daga sama. Mutanen za su fita kowace rana su tattara abin da zai ishe su na ranan. Ta haka zan gwada su in ga ko za su bi umarnaina.
And YHWH says to Moses, “Behold, I am raining bread from the heavens for you—and the people have gone out and gathered the matter of a day in its day—so that I try them whether they walk in My law or not;
5 A rana ta shida za su shirya abin da suka kwaso, wannan kuwa zai zama ninki biyu na abin da sukan tattara na sauran ranaku.”
and it has been on the sixth day, that they have prepared that which they bring in, and it has been double above that which they gather day [by] day.”
6 Saboda haka Musa da Haruna suka ce wa dukan Isra’ila, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fitar da ku daga Masar.
And Moses says—Aaron also—to all the sons of Israel, “Evening—and you have known that YHWH has brought you out from the land of Egypt;
7 Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, saboda ya ji gunaguninku a kansa. Wane mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?”
and morning—and you have seen the glory of YHWH, in His hearing your murmurings against YHWH, and what [are] we, that you murmur against us?”
8 Musa ya kuma ce, “Za ku san cewa shi ne Ubangiji, sa’ad da ya ba ku nama ku ci da yamma, da kuma duk burodin da kuke so da safe, saboda ya ji gunagunin da kuka yi a kansa. Namu a wane? Ai, gunaguninku ba a kanmu ba, amma a kan Ubangiji ne.”
And Moses says, “In YHWH’s giving to you flesh to eat in the evening, and bread in the morning to satiety—in YHWH’s hearing your murmurings, which you are murmuring against Him, and what [are] we? Your murmurings [are] not against us, but against YHWH.”
9 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ka faɗa wa dukan taron Isra’ila, ‘Ku zo gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninku.’”
And Moses says to Aaron, “Say to all the congregation of the sons of Israel, Come near before YHWH, for He has heard your murmurings”;
10 Yayinda Haruna yake magana da dukan taron Isra’ila, sai suka duba wajen hamada, sai ga ɗaukakar Ubangiji tana bayyana a girgije.
and it comes to pass, when Aaron is speaking to all the congregation of the sons of Israel, that they turn toward the wilderness, and behold, the glory of YHWH is seen in the cloud.
11 Ubangiji ya ce wa Musa,
And YHWH speaks to Moses, saying,
12 “Na ji gunagunin Isra’ilawa. Ka faɗa musu, ‘A tsakanin fāɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe kuma za ku ƙoshi da burodi. Sa’an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’”
“I have heard the murmurings of the sons of Israel; speak to them, saying, Between the evenings you eat flesh, and in the morning you are satisfied [with] bread, and you have known that I [am] your God YHWH.”
13 Da yamman wannan rana, sai makware suka rufe dukan sansani, da safe kuma sai ga raɓa ta kewaye sansani.
And it comes to pass in the evening, that the quail comes up, and covers the camp, and in the morning there has been the lying of dew around the camp,
14 Lokacin da raɓar ta watse, sai ga wani abu kamar tsaki, falle-falle kuma da laushi, fari, kamar hazo, a ƙasa.
and the lying of the dew goes up, and behold, on the face of the wilderness [is] a thin, bare thing, thin as hoarfrost on the earth.
15 Sa’ad da Isra’ilawa suka ga wannan, sai suka ce wa junansu, “Mene ne wannan?” Gama ba su san ko mene ne ba. Musa ya ce musu, “Wannan shi ne burodin da Ubangiji ya ba ku ku ci.
And the sons of Israel see, and say to one another, “What [is] it?” For they have not known what it [is]; and Moses says to them, “It [is] the bread which YHWH has given to you for food.
16 Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Kowane mutum zai tattara bisa ga bukatarsa. Ku tara rabin gallon don mutum guda da yake cikin tentinku.’”
This [is] the thing which YHWH has commanded: Gather of it, each according to his eating, an omer for the counted head; and the number of your persons, take, each, for those in his tent.”
17 Isra’ilawa suka yi kamar yadda aka faɗa musu, waɗansu suka tattara da yawa, waɗansu kuma kaɗan.
And the sons of Israel do so, and they gather, he who is [gathering] much, and he who is [gathering] little;
18 Da suka gwada a mudu, wanda ya tattara da yawa bai sami mafi yawa ba, wanda kuma ya tattara kaɗan bai sami ƙanƙani ba. Kowane mutum ya tattara daidai bukatarsa.
and they measure with an omer, and he who is [gathering] much has nothing over, and he who is [gathering] little has no lack, each according to his eating they have gathered.
19 Sa’an nan Musa ya ce musu, “Kada wani yă bar saura har safe.”
And Moses says to them, “Let no man leave of it until morning”;
20 Duk da haka waɗansu ba su kula da umarnin Musa ba, suka bar saura har safe, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su.
and they have not listened to Moses, and some of them leave of it until morning, and it brings up worms and stinks; and Moses is angry with them.
21 Kowace safiya, kowanne mutum yakan tattara daidai bukatarsa, lokacin da rana ta yi zafi, sai ta narke.
And they gather it morning by morning, each according to his eating; when the sun has been warm, then it has melted.
22 A rana ta shida, suka tattara ninki biyu, mudu biyu ga mutum guda, sai shugabannin taron suka zo suka kawo ƙara wurin Musa.
And it comes to pass on the sixth day, they have gathered a second bread, two omers for one, and all the princes of the congregation come in, and declare [it] to Moses.
23 Shi kuma ya ce musu, “Wannan shi ne umarnin Ubangiji, ‘Gobe za tă zama ranar hutu, Asabbaci mai tsarki ga Ubangiji. Domin haka sai ku toya abin da kuke so ku toya, ku kuma dafa abin da kuke so ku dafa. Abin da ya rage ku ajiye har safe.’”
And he says to them, “It [is] that which YHWH has spoken: A rest—a holy Sabbath to YHWH—[is] tomorrow; that which you bake, bake; and that which you boil, boil; and all that is remaining, let [it] rest for yourselves for preservation until the morning.”
24 Sai suka bar saura har safe, kamar yadda Musa ya umarta, bai kuwa yi wari ko yă yi tsutsa ba.
And they let it rest until the morning, as Moses has commanded, and it has not stunk, and a worm has not been in it.
25 Musa ya ce, “Ku ci shi yau, saboda yau Asabbaci ne na Ubangiji. Ba za ku same shi a ƙasa a yau ba.
And Moses says, “Eat it today, for today [is] a Sabbath to YHWH; today you do not find it in the field:
26 Kwana shida za ku tattara shi, amma a rana ta bakwai, Asabbaci, ba za a same shi ba.”
six days you gather it, and in the seventh day—the Sabbath—there is none in it.”
27 Duk da haka waɗansu mutane suka fita a ranar Asabbaci don su tattara, amma ba su sami kome ba.
And it comes to pass on the seventh day, some of the people have gone out to gather, and have not found.
28 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi bin dokokina da umarnaina?
And YHWH says to Moses, “How long have you refused to keep My commands and My laws?
29 Ku lura fa, ai, Ubangiji ne ya ba ku Asabbaci; shi ya sa a kan ba ku burodi na kwana biyu, a rana ta shida. Kowa ya kamata yă kasance inda yake a rana ta bakwai; kada kowa yă fita.”
See, because YHWH has given the Sabbath to you, therefore He is giving to you on the sixth day bread of two days; each abide [in] his place, no one goes out from his place on the seventh day.”
30 Sai mutanen suka huta a rana ta bakwai.
And the people rest on the seventh day,
31 Mutanen Isra’ila suka kira burodin Manna. Manna yana nan fari kamar farin riɗi, ɗanɗanonsa kuma yana kama da masa da aka yi da zuma.
and the house of Israel calls its name Manna, and it [is] as white coriander seed; and its taste [is] as a cake with honey.
32 Musa ya ce, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, ‘Ku auna mudu guda na Manna, a adana ta dukan zamananku, domin kowane zamani yă ga irin abincin da na ba ku ku ci a hamada, yayinda na fitar da ku daga Masar.’”
And Moses says, “This [is] the thing which YHWH has commanded: Fill the omer with it, for a charge for your generations, so that they see the bread which I have caused you to eat in the wilderness, in My bringing you out from the land of Egypt.”
33 Saboda haka Musa ya ce wa Haruna, “Ka ɗauki tulu, ka sa mudu guda na Manna a ciki. Sa’an nan ka sa shi a gaban Ubangiji, don a adana don tsararraki masu zuwa.”
And Moses says to Aaron, “Take one pot, and put the fullness of the omer of manna [in] there, and let it rest before YHWH, for a charge for your generations”;
34 Sai Haruna ya ajiye Mannar a gaban Akwatin Alkawari, don a adana ta kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
as YHWH has given command to Moses, so Aaron lets it rest before the Testimony, for a charge.
35 Isra’ilawa suka yi shekaru arba’in suna cin Manna, har sai da suka shiga cikin ƙasar da take da mutane, suka ci Manna har zuwa kan iyakar ƙasar Kan’ana.
And the sons of Israel have eaten the manna [for] forty years, until their coming to the land to be inhabited; they have eaten the manna until their coming to the extremity of the land of Canaan.
36 (Omer guda, daidai ne da kashi ɗaya bisa goma na Efa.)
And the omer is a tenth of the ephah.

< Fitowa 16 >