< Esta 6 >

1 A daren nan, sarki bai iya barci ba, saboda haka ya ba da umarni a kawo, a kuma karanta masa littafin tarihi na shekara-shekara, da rubutaccen labarin mulkinsa.
On that night the sleep of the king has fled away, and he commands to bring in the scroll of memorials of the chronicles, and they are read before the king,
2 Aka tarar, a rubuce a ciki, cewa Mordekai ya tone ƙulle-ƙullen Bigtana da Teresh, biyu daga hafsoshin sarki, waɗanda suke tsaron mashigin ƙofa, waɗanda suka ƙulla su kashe Sarki Zerzes.
and it is found written that Mordecai had declared concerning Bigthana and Teresh, two of the eunuchs of the king, of the keepers of the threshold, who sought to put forth a hand on King Ahasuerus.
3 Sarki ya ce, “Wace girma da daraja ce aka ba wa Mordekai saboda wannan?” Masu hidimarsa suka ce, “Ba a yi masa wani abu ba.”
And the king says, “What honor and greatness has been done to Mordecai for this?” And the servants of the king, his ministers, say, “Nothing has been done with him.”
4 Sarki ya ce, “Wa yake a haraba?” Daidai lokacin kuwa Haman ya shigo harabar waje na fada don yă yi magana da sarki a kan a rataye Mordekai a wurin rataye mai laifin da ya shirya.
And the king says, “Who [is] in the court?” And Haman has come into the outer court of the house of the king, to say to the king to hang Mordecai on the tree that he had prepared for him.
5 Masu yi wa sarki hidima, suka amsa, “Haman yana tsaye a haraba.” Sarki ya umarta, “A kawo shi ciki.”
And the servants of the king say to him, “Behold, Haman is standing in the court”; and the king says, “Let him come in.”
6 Sa’an nan Haman ya shigo, sai sarki ya ce masa, “Me ya kamata a yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama?” Haman dai ya yi tunani a ransa ya ce, “Wane ne sarki zai girmama in ba ni ba?”
And Haman comes in, and the king says to him, “What should [I] do with the man in whose honor the king has delighted?” And Haman says in his heart, “To whom does the king delight to do honor more than myself?”
7 Sai ya amsa wa sarki cewa, “Saboda mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama,
And Haman says to the king, “The man in whose honor the king has delighted,
8 bari a kawo rigar sarautar da sarki ya taɓa sawa, da kuma dokin da sarki ya taɓa hawa, wanda aka sa kambin sarauta a kai.
let them bring in royal clothing that the king has put on himself, and a horse on which the king has ridden, and that the royal crown be put on his head,
9 Sa’an nan, bari a ba da rigar da kuma dokin wa ɗaya daga cikin manyan sarakuna mafi kirki na sarki. Bari shi kuma yă sa wannan riga wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama, a kuma bi da shi a bisan doki ko’ina a titunan birni, ana shela a gabansa ana cewa, ‘Wannan shi ne abin da ake yin wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama!’”
and to give the clothing and the horse into the hand of a man of the heads of the king, the chiefs, and they have clothed the man in whose honor the king has delighted, and caused him to ride on the horse in a broad place of the city, and called before him: Thus it is done to the man in whose honor the king has delighted.”
10 Sarki ya umarci Haman ya ce, “Tafi yanzu ka karɓi rigar da dokin, ka kuma yi yadda ka shawarta wa Mordekai, mutumin Yahudan nan, wanda yake zama a bakin ƙofar sarki. Kada ka kāsa yin kome daga cikin abin da ka faɗa.”
And the king says to Haman, “Hurry, take the clothing and the horse, as you have spoken, and do so to Mordecai the Jew, who is sitting in the gate of the king; there does not fall a thing of all that you have spoken.”
11 Saboda haka, Haman ya karɓo rigar da dokin. Ya sa wa Mordekai rigar, ya kuma bi da shi a kan doki ko’ina a titunan birnin, yana shela a gabansa yana cewa, “Wannan shi ne abin da ake yi wa mutumin da sarki yake jin daɗi yă girmama!”
And Haman takes the clothing, and the horse, and clothed Mordecai, and causes him to ride in a broad place of the city, and calls before him, “Thus it is done to the man in whose glory the king has delighted.”
12 Daga baya, Mordekai ya dawo zuwa ƙofar sarki. Amma Haman ya ruga gida, kansa a rufe, saboda baƙin ciki.
And Mordecai turns back to the gate of the king, and Haman has been hurried to his house mourning, and with covered head,
13 Ya je ya faɗa wa matarsa Zeresh, da dukan abokansa, me ya same shi. Masu ba shi shawara, da matarsa Zeresh, suka ce masa, “Idan Mordekai, wanda ka fara fāɗuwa a gabansa, daga zuriyar Yahudawa yake, to, ba za ka yi nasara a kansa ba, tabbatacce za ka fāɗi a gabansa!”
and Haman recounts to his wife Zeresh, and to all his friends, all that has met him, and his wise men and his wife Zeresh say to him, “If Mordecai [is] of the seed of the Jews, before whom you have begun to fall, you are not able for him, but certainly fall before him.”
14 Suna cikin magana da shi ke nan, sai ga bābānnin sarki, suka iso suka kuma hanzarta da Haman zuwa liyafar da Esta ta shirya.
They are yet speaking with him, and eunuchs of the king have come, and hurry to bring in Haman to the banquet that Esther has made.

< Esta 6 >