< Afisawa 1 >

1 Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa, da kuma suke amintattu cikin Kiristi Yesu.
Paul, the apostle of Jesus Christ through the will of God, to the saints who are in Ephesus, and to the faithful in Christ Jesus.
2 Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
Grace to you and peace from God our Father, and the Lord Jesus Christ.
3 Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama.
Blessed is the God and Father of our Lord Jesus Christ, the one having blessed us with all spiritual blessing in the heavenlies in Christ:
4 Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa.
as he elected us in himself before the foundation of the world, that we should be holy and blameless in his presence.
5 A cikin ƙauna, ya ƙaddara mu zama’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri.
in love having predestinated us unto the adoption of sons unto himself through Jesus Christ, according to the good pleasure of his will,
6 Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne.
unto the praise of the glory of his grace, with which he has blessed us in the Beloved:
7 A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah
in whom we have redemption through his blood, the remission of transgressions, according to the riches of his grace,
8 wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta.
which he has abounded unto us in all wisdom and understanding,
9 Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi.
having made known unto us the mystery of his will, according to his own good pleasure, which he purposed in himself
10 Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.
in the economy of the fulness of the times, to rehead all things in Christ, those in the heavens, and those upon the earth; in him,
11 A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi.
in whom we were also chosen by lot, having been predestinated according to the purpose of him who works all things within us according to the counsel of his own will;
12 Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah.
that we should be unto the praise of his glory, who first exercised hope in Christ:
13 An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki.
in whom you also, having heard the word of truth, the gospel of your salvation, in whom, also having believed, you were sealed with the Holy Spirit of promise,
14 Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.
who is the earnest of our salvation, unto the redemption of the possession, unto the praise of his glory.
15 Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah,
Therefore I also, having heard of the faith among you in the Lord Jesus, and your love which is toward all the saints,
16 ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina.
I do not cease giving thanks for you making mention of you in my prayers;
17 Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau.
in order that the God of our Lord Jesus Christ, the Father of the glory, may grant unto you the spirit of wisdom and of revelation in the perfect knowledge of himself;
18 Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa.
the eyes of your heart having been enlightened, that you may know what is the hope of his calling, what the riches of the glory of his inheritance among the saints,
19 Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan
and what the excellent majesty of his power toward us who believe, according to the working of the power of his might
20 da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya.
which he has wrought in Christ, raising him from the dead, and seating him on his right hand in the heavenlies,
21 Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. (aiōn g165)
above all government, and authority, and power, and lordship, and every name named, not only in this age, but in the age to come: (aiōn g165)
22 Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya.
and has subordinated all things beneath his feet, and given him to be head over all things to the church,
23 Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.
which is his body, the fulness of him who fills all things in all.

< Afisawa 1 >