< Mai Hadishi 1 >

1 Kalmomin Malami, ɗan Dawuda, Sarki a Urushalima.
Words of a preacher, son of David, king in Jerusalem:
2 “Ba amfani! Ba amfani!” In ji Malami. “Gaba ɗaya ba amfani! Kome ba shi da amfani!”
Vanity of vanities, said the Preacher, vanity of vanities: the whole [is] vanity.
3 Wace riba ce mutum yake samu daga wahalar da yake fama a duniya?
What advantage [is] to man by all his labor that he labors at under the sun?
4 Zamanai sukan zo zamanai su wuce, amma duniya tana nan har abada.
A generation is going, and a generation is coming, and the earth is standing for all time.
5 Rana takan fito rana ta kuma fāɗi, ta kuma gaggauta zuwa inda takan fito.
Also, the sun has risen, and the sun has gone in, and to its place panting it is rising there.
6 Iska takan hura zuwa kudu ta kuma juya zuwa arewa; tă yi ta kewayewa, tă yi ta koma inda take fitowa.
Going to the south, and turning around to the north, turning around, turning around, the wind is going, and by its circuits the wind has returned.
7 Dukan rafuffuka sukan gangara zuwa teku, duk da haka teku ba ya cika. Daga inda rafuffukan suke fitowa, a can suke komawa kuma.
All the streams are going to the sea, and the sea is not full; to a place to where the streams are going, there they are turning back to go.
8 Dukan abubuwa suna kawo gajiya, gaban magana. Ido ba ya gaji da gani, haka ma kunne yă ƙoshi da ji.
All these things are wearying; a man is not able to speak, the eye is not satisfied by seeing, nor is the ear filled from hearing.
9 Abin da ya taɓa kasancewa, zai sāke kasance, abin da aka yi za a sāke yi kuma; babu wani abu sabo a duniya.
What [is] that which has been? It [is] that which is, and what [is] that which has been done? It [is] that which is done, and there is not an entirely new thing under the sun.
10 Akwai wani abin da za a ce, “Duba! Ga wani abu sabo”? Abin yana nan, tun dā can, ya kasance kafin lokacinmu.
There is a thing of which [one] says: “See this, it [is] new!” Already it has been in the ages that were before us!
11 Ba a tunawa da mutanen dā, haka su ma da ba a haifa ba tukuna waɗanda za su biyo bayansu ba za a tuna da su ba.
There is not a remembrance of former [generations]; and also of the latter that are, there is no remembrance of them with those that are at the last.
12 Ni, Malami, sarki ne bisa Isra’ila a Urushalima.
I, a preacher, have been king over Israel in Jerusalem.
13 Na dauri aniyata in gwada don in bincika ta wurin hikima dukan abin da ake yi a duniya. Kaya mai nauyi ne Allah ya ɗora a kan mutane!
And I have given my heart to seek and to search out by wisdom concerning all that has been done under the heavens. It [is] a sad travail God has given to the sons of man to be humbled by it.
14 Na ga dukan abubuwan da ake yi a duniya, dukansu ba su da amfani, naushin iska ne kawai.
I have seen all the works that have been done under the sun, and behold, the whole [is] vanity and distress of spirit!
15 Abin da yake tanƙwararre ba zai miƙu ba; ba za a kuma iya ƙidaya abin da ba shi ba.
A crooked thing [one] is not able to make straight, and a lacking thing is not able to be numbered.
16 Na yi tunani a raina na ce, “Duba, na yi girma, na kuma ƙaru da hikima fiye da duk wanda ya taɓa mulki a bisa Urushalima kafin ni; na ɗanɗana hikima mai yawa da kuma ilimi.”
I spoke with my heart, saying, “I, behold, have magnified and added wisdom above everyone who has been before me at Jerusalem, and my heart has seen wisdom and knowledge abundantly.
17 Sa’an nan na ɗaura aniyata ga fahimtar hikima, in kuma san bambanci tsakanin hauka da wauta, amma na koyi cewa wannan ma, naushin iska ne kawai.
And I give my heart to know wisdom, and to know madness and folly: I have known that even this [is] distress of spirit;
18 Gama yawan hikima yakan kawo yawan baƙin ciki; yawan sani, yawan ɓacin rai.
for in abundance of wisdom [is] abundance of sadness, and he who adds knowledge adds pain.”

< Mai Hadishi 1 >