< Maimaitawar Shari’a 7 >

1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya kawo ku ƙasar da kuke shiga don ku mallaka, ya kuma kori al’ummai masu yawa a gabanku; wato, Hittiyawa, Girgashiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa, al’ummai bakwai masu girma da ƙarfi fiye da ku.
Lorsque Yahweh, ton Dieu, t’aura fait entrer dans le pays dont tu vas prendre possession, et qu’il aura chassé devant toi beaucoup de nations, les Hittites, les Gergéséens, les Amorrhéens, les Chananéens, les Phéréséens, les Hévéens et les Jébuséens, sept nations plus nombreuses et plus puissantes que toi,
2 Sa’ad da kuma Ubangiji Allahnku ya ba da su gare ku, kuka kuma ci su da yaƙi, sai ku hallaka su ƙaƙaf. Kada ku yi yarjejjeniya da su, kada kuma ku nuna musu jinƙai.
et que Yahweh, ton Dieu, te les aura livrées et que tu les auras battues, tu les dévoueras par anathème, tu ne concluras pas d’alliance avec elles et tu ne leur feras pas grâce.
3 Kada ku yi auratayya da su. Kada ku ba da’ya’yanku mata wa’ya’yansu maza, ko ku ɗauko’ya’yansu mata wa’ya’yanku maza.
Tu ne contracteras pas de mariage avec elles, tu ne donneras pas tes filles à leurs fils, et tu ne prendras pas leurs filles pour tes fils;
4 Gama za su juye’ya’yanku maza daga bina, su bauta waɗansu alloli, fushin Ubangiji kuma zai ƙuna a kanku da sauri, zai kuma hallaka ku.
car elles détourneraient de marcher après moi tes fils, qui serviraient d’autres dieux; la colère de Yahweh s’enflammerait contre vous, et il te détruirait promptement.
5 Ga abin da za ku yi da su, za ku rurrushe bagadansu, ku ragargaza keɓaɓɓun duwatsunsu, ku farfashe ginshiƙan Asheransu, ku kuma ƙona gumakansu da wuta.
Mais voici comment vous agirez à leur égard: Vous renverserez leurs autels, vous briserez leurs stèles, vous abattrez leurs aschérim et vous livrerez au feu leurs images taillées.
6 Gama ku mutane masu tsarki ne ga Ubangiji Allahnku. Ubangiji Allahnku ya zaɓe ku daga dukan mutane a fuskar duniya, don ku zama mutanensa, kayan gādonsa.
Car tu es un peuple saint à Yahweh, ton Dieu. Yahweh, ton Dieu, t’a choisi pour être son peuple particulier, parmi tous les peuples qui sont sur la face de la terre.
7 Ba don kun fi sauran al’ummai yawa ne ya sa Ubangiji ya ƙaunace ku, ya kuma zaɓe ku ba, gama ku ne mafi ƙanƙanta cikin dukan al’ummai.
Si Yahweh s’est attaché à vous et vous a choisis, ce n’est pas que vous surpassiez en nombre tous les peuples, car vous êtes le plus petit de tous les peuples.
8 Amma ya zama haka domin Ubangiji ya ƙaunace ku, ya kuma kiyaye rantsuwar da ya yi wa kakanninku da ya fitar da ku da hannu mai ƙarfi, ya kuma cece ku daga ƙasar bauta, daga ikon Fir’auna sarkin Masar.
Mais, parce que Yahweh vous aime et parce qu’il a voulu tenir le serment qu’il avait fait à vos pères, Yahweh vous a fait sortir par sa main puissante et vous a rachetés de la maison de servitude, de la main de Pharaon, roi d’Égypte.
9 Saboda haka, ku sani cewa Ubangiji Allahnku, shi ne Allah; shi Allah ne mai aminci, yana kiyaye alkawarinsa na ƙauna ga tsararraki dubu na waɗanda suke ƙaunarsa suke kuma kiyaye umarnansa.
Sache donc que c’est Yahweh, ton Dieu, qui est Dieu, le Dieu fidèle qui garde l’alliance et la miséricorde jusqu’à mille générations, pour ceux qui l’aiment et qui gardent ses commandements.
10 Amma waɗanda suke ƙinsa, a fili yakan sāka musu da hallaka; ba zai yi jinkiri yin ramuwa a kan maƙiyinsa ba, zai yi ramuwar a fili.
Mais il rend la pareille en face à ceux qui le haïssent, en les faisant périr; il ne tarde pas à l’égard de celui qui le hait, et il lui rend la pareille en face.
11 Saboda haka, sai ku lura, ku bi umarnai, ƙa’idodi, da dokokin nan da nake ba ku a yau.
C’est pourquoi tu observeras les commandements, les lois et les ordonnances que je te prescris aujourd’hui, en les mettant en pratique.
12 In kuka mai da hankali ga waɗannan dokoki, kuka kuma yi hankali ga bin su, to, Ubangiji Allahnku zai kiyaye alkawarinsa na ƙauna gare ku, kamar yadda ya rantse wa kakanninku.
Si vous écoutez ces ordonnances, si vous les gardez et les mettez en pratique, en retour Yahweh, ton Dieu, gardera envers toi l’alliance et la miséricorde qu’il a jurées à tes pères.
13 Zai ƙaunace ku, yă albarkace ku, yă kuma ƙara yawanku. Zai albarkaci’ya’yanku, amfanin gonarku; hatsinku, sabon ruwan inabinku da kuma mai, ƙanana shanunku, da’yan tumaki na tumakinku, a ƙasar da ya rantse wa kakanninku cewa zai ba ku.
Il t’aimera, te bénira et te multipliera; il bénira le fruit de tes entrailles et le fruit de ton sol, ton blé, ton vin nouveau et ton huile, les portées de tes vaches et les petits de tes brebis, sur la terre qu’il a juré à tes pères de te donner.
14 Za a albarkace ku fiye da waɗansu mutane; babu wani cikin maza ko matanku da zai kasance babu haihuwa, ba kuwa wata dabbarku da za tă kasance babu haihuwa.
Tu seras béni plus que tous les peuples; il n’y aura chez toi ni homme ni femme stérile, ni bête stérile parmi tes troupeaux.
15 Ubangiji zai kiyaye ku daga kowace cuta. Ba zai wahalshe ku da mugayen cututtukan da kuka sani a Masar ba, amma zai aukar wa dukan maƙiyanku.
Yahweh éloignera de toi toute maladie; il ne t’enverra aucune de ces affections malignes d’Égypte que tu connais; mais il en affligera tous ceux qui te haïssent.
16 Dole ku hallaka dukan mutanen da Ubangiji Allahnku ya bashe su gare ku. Kada ku ji tausayinsu, kada kuma ku bauta wa allolinsu, gama wannan zai zama tarko gare ku.
Tu dévoreras tous les peuples que Yahweh, ton Dieu, va te livrer; ton œil sera sans pitié pour eux, et tu ne serviras pas leurs dieux, car ce serait un piège pour toi.
17 Wataƙila ku ce wa kanku, “Waɗannan al’ummai sun fi mu ƙarfi. Yaya za mu kore su?”
Que si tu dis dans ton cœur: « Ces nations sont plus nombreuses que moi; comment pourrai-je les chasser? »
18 Amma kada ku ji tsoronsu; ku tuna da kyau abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Fir’auna da kuma dukan Masar.
Ne les crains pas; rappelle à ton souvenir ce que Yahweh, ton Dieu, a fait à Pharaon et à toute l’Égypte:
19 Kun ga da idanunku, manyan gwaje-gwaje, alamu masu banmamaki da al’ajabai, hannu mai ƙarfi da kuma mai ikon da Ubangiji Allahnku ya fitar da ku. Ubangiji Allahnku zai yi haka ga dukan mutanen da yanzu kuke tsoro.
les grandes épreuves que tes yeux ont vues, les miracles et les prodiges, la main forte et le bras étendu, par lesquels Yahweh, ton Dieu, t’a fait sortir: ainsi fera Yahweh, ton Dieu, à tous les peuples dont tu as peur.
20 Ban da haka ma, Ubangiji Allahnku zai aika da rina a cikinsu, har sai sun hallaka sauran mutanen da suka ragu, waɗanda suka ɓuya daga gare ku.
Yahweh, ton Dieu, enverra même sur eux les frelons, jusqu’à ce que soient détruits ceux qui auront pu échapper et se cacher devant toi.
21 Kada ku tsorata saboda su, gama Ubangiji Allahnku, wanda yake a cikinku, Allah ne mai girma da kuma mai banrazana.
Tu ne t’effraieras pas à cause d’eux; car Yahweh, ton Dieu, est au milieu de toi, Dieu grand et terrible!
22 Da kaɗan da kaɗan Ubangiji Allahnku zai kore waɗannan al’ummai a gabanku. Ba a bari ku hallaka su duka gaba ɗaya ba, in ba haka namun jeji za su yaɗu kewaye da ku.
Yahweh, ton Dieu, chassera peu à peu ces nations devant toi; tu ne pourras pas les exterminer promptement, de peur que les bêtes sauvages ne se multiplient contre toi.
23 Amma Ubangiji Allahnku zai ba da su gare ku, yana jefa su cikin rikicewa mai girma, har sai an hallaka su.
Yahweh, ton Dieu, te les livrera, et il jettera parmi elles une grande consternation, jusqu’à ce qu’elles soient détruites.
24 Zai ba da sarakunsu a hannunku, za ku kuwa shafe sunayensu daga duniya. Babu wani da zai yi tsayayya da ku, za ku hallaka su.
Il livrera leurs rois entre tes mains et tu feras disparaître leurs noms de dessous les cieux; personne ne tiendra devant toi, jusqu’à ce que tu les aies détruits.
25 Ku ƙone siffar allolinsu da wuta. Kada ku yi ƙyashin azurfa ko zinariyar da aka rufe allolin da ita, Kada ku kwashe su, don kada su zamar muku tarko, gama abin ƙyama ne ga Ubangiji Allahnku.
Vous consumerez par le feu les images taillées de leurs dieux; tu ne convoiteras pas l’argent ou l’or qui est sur elles, et tu ne le prendras pas pour toi, de peur qu’il ne te soit un piège; car il est en abomination à Yahweh, ton Dieu.
26 Kada ku kawo abin ƙyama cikin gidajenku, domin kada ku zama kamar su. Gaba ɗaya ku yi ƙyamarsu, ku ƙi su, gama an ware su, sun zama domin a hallaka.
Tu n’introduiras pas une chose abominable dans ta maison, afin que tu ne sois pas, comme elle, dévoué par anathème; tu l’auras en horreur extrême, tu l’auras en extrême abomination, car c’est une chose dévouée par anathème.

< Maimaitawar Shari’a 7 >