< Maimaitawar Shari’a 33 >
1 Wannan ita ce albarkar da Musa mutumin Allah ya furta a kan Isra’ilawa, kafin yă rasu.
Or, voici la bénédiction dont Moïse, l’homme de Dieu, bénit les enfants d’Israël avant de mourir.
2 Ya ce, “Ubangiji ya zo daga Sinai ya haskaka a bisansu daga Seyir; ya haskaka daga Dutsen Faran. Ya zo tare da dubban tsarkakansa daga kudu, daga gangara dutsensa.
Il dit: "L’Éternel est apparu du haut du Sinaï, a brillé sur le Séir, pour eux! S’Est révélé sur le mont Pharan, a quitté les saintes myriades qui l’entourent, dans sa droite une loi de feu, pour eux!
3 Tabbatacce kai ne wanda yake ƙaunar mutane; dukan tsarkaka suna a hannunka. A ƙafafunka, duk suka rusuna, daga wurinka kuma suka karɓi umarni,
Ils te sont chers aussi, les peuples; tous leurs saints, ta main les protège: mais eux se sont couchés à tes pieds, ont recueilli ta propre parole.
4 dokar Musa ta ba mu dokoki, mallakar taron Yaƙub.
"C’Est pour nous qu’il dicta une doctrine à Moïse; elle restera l’héritage de la communauté de Jacob."
5 Shi ne sarki a bisa Yeshurun sa’ad da shugabannin mutane suka taru, tare da kabilan Isra’ila.
Ainsi devint-il roi de Yechouroun, les chefs du peuple étant réunis, les tribus d’Israël unanimes.
6 “Bari Ruben yă rayu, kada yă mutu, kada mutanensa su zama kaɗan.”
"Que Ruben vive et soit immortel; que sa population soit innombrable!
7 Ya kuma faɗa wannan game da Yahuda, “Ka ji, ya Ubangiji, kukan Yahuda; ka kawo shi wurin mutanensa. Da hannuwansa ya kāre kansa. Ka taimake shi a kan maƙiyansa!”
A Juda, il adressa cette bénédiction: "Ecoute, Seigneur, le vœu de Juda, en l’associant à son peuple; que son bras s’en fasse le champion et lui serve d’auxiliaire contre ses ennemis."
8 Game da Lawi ya ce, “Tummim da Urim na mutumin da ka nuna masa tagomashi ne. Ka gwada shi a Massa; ka yi faɗa da shi a ruwan Meriba.
Sur Lévi, il s’exprima ainsi: "Tes toummîm et tes ourîm à l’homme qui t’est dévoué; que tu as éprouvé à Massa, gourmandé pour les eaux de Meriba;
9 Ya yi zancen mahaifinsa da mahaifiyarsa ya ce, ‘Ban kula da su ba.’ Bai gane da’yan’uwansa ba, ko yă yarda da’ya’yansa, amma ya kiyaye maganarka ya tsare alkawarinka.
qui dit de son père et de sa mère: "Je ne les considère point", qui n’a pas égard à ses frères et ne connaît pas ses enfants. Uniquement fidèle à ta parole, gardien de ton alliance,
10 Ya koyar da farillanka ga Yaƙub, dokarka kuma ga Isra’ila. Ya miƙa turare a gabanka da kuma hadaya ta ƙonawa ɗungum a kan bagadenka.
ils enseignent tes lois à Jacob et ta doctrine à Israël; présentent l’encens devant ta face, et l’holocauste sur ton autel.
11 Ka albarkaci ɗaukan dabarunsa, ya Ubangiji, ka kuma ji daɗin aikin hannuwansa. Ka murƙushe kwankwaso waɗanda suka tayar masa; ka bugi abokan gābansa har sai ba su ƙara tashi ba.”
Bénis, Seigneur, ses efforts, et agrée l’œuvre de ses mains! Brise les reins de ses agresseurs, de ses ennemis, pour qu’ils ne puissent se relever!
12 Game da Benyamin ya ce, “Bari ƙaunataccen Ubangiji yă zauna lafiya kusa da shi, gama yana tsare shi dukan yini, wanda kuma Ubangiji yake ƙauna yana zama a tsakanin kafaɗunsa.”
Sur Benjamin, il dit: "Favori du Seigneur, il repose avec confiance auprès de lui, qui lui prête son abri pour toujours et qui réside entre ses épaules."
13 Game da Yusuf ya ce, “Bari Ubangiji yă albarkaci ƙasarsa da raɓa mai daraja daga sama a bisa da kuma zurfin ruwan da suke kwance a ƙarƙashi;
Sur Joseph, il parla ainsi: "Bénie du Seigneur est sa terre! Elle possède les dons du ciel, la rosée, comme ceux de l’abîme aux couches souterraines:
14 da abubuwa masu kyau da rana take kawo, da kuma abubuwa mafi kyau da wata zai iya haifar;
et les trésors que mûrit le soleil, et ceux qui germent à chaque lune;
15 da zaɓaɓɓun kyautai na daɗaɗɗun duwatsu, da kyawawan amfani na madawwaman tuddai.
et les précieux produits des antiques montagnes, et les délices des collines primitives,
16 Tare da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, da tagomashi na wanda yake zama a ƙaramin itace mai ƙonewa. Bari duk waɗannan su zauna a kan Yusuf, a goshin sarki a cikin’yan’uwansa.
les délices du sol et son abondance, et la faveur de celui qui eut pour trône un buisson. Puisse-t-elle reposer sur la tête de Joseph, sur le front de l’élu de ses frères!
17 Cikin daraja yana yi kamar ɗan fari na bijimi; ƙahoninsa ƙahonin ɓauna ne. Tare da su zai tukwiyi al’ummai, har ma da waɗanda suke ƙarshen duniya. Haka dubu dubban Efraim suke; haka dubban Manasse suke.”
Le taureau, son premier-né qu’il est majestueux! Ses cornes sont celles du reêm: avec elles il terrassera les peuples, tous ensemble jusqu’aux confins de la terre. L’Une, ce sont les myriades d’Ephraïm, l’autre, les milliers de Manassé!"
18 Game da Zebulun ya ce, “Ka yi farin ciki, Zebulun, a fitowarka, kai kuma Issakar, a cikin tentunanka.
A Zabulon, il dit ces mots: "Sois heureux, Zabulon, dans tes voyages, et toi, Issachar, dans tes tentes!
19 Za su kira mutane zuwa dutse, a can za su miƙa hadayun adalci; za su yi biki a yalwan tekuna, a dukiyoyin da aka ɓoye a cikin yashi.”
Ils convieront des peuples sur la montagne, pour y offrir des sacrifices pieux; car ils aspireront l’opulence des mers et les mystérieux trésors cachés dans le sable."
20 Game da Gad ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fadada mazaunin Gad! Gad yana zama a can kamar zaki, yana yayyage a hannu da kai.
Au sujet de Gad, il dit: "Hommage à celui qui agrandit Gad! Il se campe comme un léopard, met en pièces et le bras et la tête.
21 Ya zaɓi ƙasa mafi kyau wa kansa; aka ajiye masa rabon shugaba. Sa’ad da shugabannin mutane suka taru, ya aikata adalcin Ubangiji da kuma hukuncinsa game da Isra’ila.”
Il s’est adjugé les prémices de la conquête, là est sa part, réservée par le législateur: il s’avance cependant aux premiers rangs du peuple, accomplissant l’œuvre sainte du Seigneur, fidèle à ses devoirs envers Israël!"
22 Game da Dan ya ce, “Dan ɗan zaki ne, yana tsalle daga Bashan.”
Au sujet de Dan, il dit: "Dan est un jeune lion qui s’élance du Basan."
23 Game da Naftali ya ce, “Naftali ƙosasshe ne da tagomashin Ubangiji, ya kuma cika albarkarsa; zai gāji gefen kudu zuwa tafki.”
A Nephtali, il dit: "Ô Nephtali! Rassasié des grâces diverses, comblé des bénédictions du Seigneur, que le couchant et le midi soient ton héritage!"
24 Game da Asher ya ce, “Mafi albarka na’ya’yan, shi ne Asher; bari yă sami tagomashi daga’yan’uwansa, bari kuma yă wanke ƙafafunsa a cikin mai.
Et au sujet d’Asher, il dit: "Béni entre les fils soit Asher! Bienvenu auprès de ses frères, et baignant son pied dans l’huile.
25 Madogaran ƙofofinka za su zama ƙarfe da tagulla, ƙarfinka kuma zai zama daidai da kwanakinka.
Tes forts seront bardés de fer et d’airain; ta sécurité durera autant que ta vie.
26 “Babu wani kamar Allah na Yeshurun, wanda yake hawa a bisa sammai don yă taimake ka a kan gizagizai kuma a cikin darajarsa.
"Rien n’égale le Tout-Puissant, ô Yechouroun! II est ton soutien, lui qui siège dans les cieux et dont la majesté plane sur les nues.
27 Allah madawwami shi ne mafakarka, a ƙarƙashina kuma madawwamin hannuwa ne. Zai kore abokin gābanka a gabanka, yana cewa, ‘Ka hallaka shi!’
Tu as pour refuge le Dieu primordial, pour support, ses bras éternels il écarte devant toi l’ennemi. II décrète sa ruine.
28 Haka Isra’ila zai zauna lafiya shi kaɗai; zuriyar Yaƙub a tsare a ƙasar hatsi da sabon ruwan inabi, inda sammai za su zuba raɓa.
Et Israël réside avec sécurité, elle coule solitaire la source de Jacob, sur une terre riche de blé et de vin, sous des cieux qui lui versent la rosée.
29 Kai mai albarka ne, ya Isra’ila! Wane ne yake kamar ka, mutanen da Ubangiji ya ceta? Shi ne mafakarka da mai taimakonka da kuma takobinka mai ɗaukaka. Abokan gābanka za su zo neman jinƙai a gabanka, za ka kuwa tattake masujadansu.”
Heureux es-tu, Israël! Qui est ton égal, peuple que protège le Seigneur? Bouclier qui te sauve, il est aussi le glaive qui te fait triompher: tes ennemis ramperont devant toi, et toi, tu fouleras leurs hauteurs."