< Maimaitawar Shari’a 26 >

1 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta,
“After you occupy the land that Yahweh our God is giving to you, and you (have settled/are living) there,
2 sai ku ɗauki’ya’yan fari na dukan amfanin gonar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku zuba a kwando. Sa’an nan ku je wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa yă zama mazauni don Sunansa,
[each of] you must take some of the first crops that you harvest, put them in a basket, and take them to the place that Yahweh will have chosen for you to worship [MTY] there.
3 ku faɗa wa firist da yake aiki a lokacin, “Na sakankance yau ga Ubangiji Allahnka, cewa na zo ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninmu.”
Go to the Supreme Priest who is serving at that time and say to him, ‘[By giving you this first part of my harvest] today, I am declaring to Yahweh our God that I have [picked it in] the land that he vowed to our ancestors to give to us.’
4 Firist ɗin zai karɓi kwandon daga hannuwanku yă sa shi a ƙasa a gaban bagaden Ubangiji Allahnku.
Then the priest must take the basket of food from your hand and put it on the altar where sacrifices are offered to Yahweh our God.
5 Sa’an nan za ku furta a gaban Ubangiji Allahnku cewa, “Mahaifina mutumin Aram ne mai yawo, ya gangara zuwa Masar da mutane kaɗan, ya zauna a can, ya kuma zama babban al’umma, mai iko da kuma mai yawa.
Then in Yahweh’s presence you must say this: ‘My ancestor [Jacob] was a man from Aram/Syria who was continually wandering [from one place to another]. He took his family to Egypt. They were a small group [when they went there], but they lived there and their descendants became a very large/populous [DOU] and powerful nation.
6 Amma Masarawa suka wulaƙanta mu suka sa muka sha wahala, suna sa mu aikin dole.
Then the people of Egypt treated them very harshly [DOU], and they forced them to become their slaves and to work very hard.
7 Sai muka yi kuka ga Ubangiji Allahn kakanninmu, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya kuma azabar da muke sha, da wahalar da muke sha, da danniyar da suke yin mana.
Then our ancestors cried out to you, Yahweh our God, and you heard them. You saw that they were suffering, and that they were forced to work very hard, and were being oppressed.
8 Sai Ubangiji ya fitar da mu daga Masar da hannu mai ƙarfi da kuma iko, da razana mai girma da kuma alamu banmamaki da al’ajabai.
Then by your great power [MTY] and by performing many kinds of miracles [DOU], and other terrifying things, you brought them out of Egypt.
9 Ya kawo mu wannan wuri, ya kuma ba mu wannan ƙasa, ƙasa mai zub da madara da kuma zuma;
You brought us to this land and gave it to us, a land that is very fertile [IDM].
10 yanzu kuwa na kawo’ya’yan fari na gonar da kai, ya Ubangiji ka ba ni.” Sai ku sa kwandon a gaban Ubangiji Allahnku, sa’an nan ku rusuna a gabansa.
So now, Yahweh, I have brought to you the first part of the harvest from the land that I received.’ Then you must set the basket down in Yahweh’s presence and worship him there.
11 Ku da Lawiyawa da baƙin da suke a cikinku, za ku yi murna cikin dukan abubuwa masu kyau da Ubangiji Allahnku ya ba ku tare da gidanku.
And you must celebrate [by eating a meal together to thank] Yahweh our God for all the good things that he has given to you and to your family. And you must invite the descendants of Levi and the foreigners who are living among you to also rejoice [and eat] with you.
12 Sa’ad da kuka gama fitar da kashi ɗaya bisa goma na dukan amfanin gona a shekara ta uku, shekarar zakka, za ku ba da su ga Balawe, baƙo, maraya da kuma gwauruwa, don su ci a cikin garuruwanku su ƙoshi.
Every third year, you must bring to the descendants of Levi and to the foreigners [who are living among you] and the orphans and the widows (a tithe/10 percent) of your crops, in order that in every town they will have plenty to eat.
13 Sa’an nan ku faɗa wa Ubangiji Allahnku, “Na cire tsattsarkan rabo daga gidana na kuma ba wa Balawe, baƙo, maraya da gwauruwa, bisa ga dukan abin da ka umarta. Ban ja gefe daga umarnanka ko in manta da wani a cikinsu ba.
Then you must say to Yahweh, ‘I have brought to you, from my house, all of the sacred tithe [from my harvest this year]. I am giving it to the descendants of Levi, to the foreigners, the orphans, and the widows, as you commanded us to do. I have not disobeyed any of your commands [about the tithes], and I have not forgotten any of your commands [about tithes].
14 Ban ci wani daga cikin tsattsarkan rabo yayinda nake makoki, ko in cire wani rabo mai tsarki yayinda nake marar tsarki, ko in miƙa wani sashensa ga matattu ba. Na yi biyayya ga Ubangiji Allahna, na aikata kome da ka umarce ni.
[I declare that] I have not eaten any food from the tithe while I was mourning [for someone who died]. And I have not touched any of it while I was unacceptable to you; I have not offered any of it to [spirits of] dead people. Yahweh, I have obeyed you and done everything that you have commanded us [concerning the tithe].
15 Ka duba ƙasa daga sama, mazauninka mai tsarki, ka albarkace mutanenka Isra’ila da kuma ƙasar da ka ba mu kamar yadda ka yi wa kakanninmu alkawari da rantsuwa, ƙasa mai zub da madara da zuma.”
So [please] look down from your holy place in heaven, and bless us, your Israeli people. Also bless this very fertile [IDM] land which you have given to us, which is what you promised our ancestors that you would do.’
16 Yau Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi waɗannan ƙa’idodi da kuma dokoki, cikin natsuwa ku kiyaye su da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
Today Yahweh our God is commanding you to obey all these rules and regulations. So obey them faithfully, with your entire inner being [DOU].
17 Kun furta a wannan rana cewa Ubangiji shi ne Allahnku, cewa za ku kuma yi tafiya a hanyoyinsa, cewa za ku kiyaye ƙa’idodinsa, umarnansa da kuma dokokinsa, kuka kuma ce za ku yi masa biyayya.
Today you have declared that Yahweh is your God, and that you will conduct your lives as he wants you to do, and that you will obey all his commands and rules and regulations, and that you will do all that he tells you to do.
18 Ubangiji kuwa ya furta a wannan rana cewa ku mutanensa ne, mallakarsa kamar yadda ya yi alkawari, da kuma cewa za ku kiyaye dukan umarnansa.
And today Yahweh has declared that you are his people, which is what he promised that you would be, and he commands you to obey all his commands.
19 Ya furta cewa zai sa ku zama masu yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al’umman da ya yi. Za ku zama jama’a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku, kamar yadda ya yi alkawari.
If you do that, he will cause you to become greater than any other nation that he has established, and he will enable you to praise him and honor him [DOU]. You will truly belong to Yahweh our God, which is what he has promised.”

< Maimaitawar Shari’a 26 >