< Maimaitawar Shari’a 25 >
1 Idan mūsu ya tashi tsakanin mutum biyu har abin ya kai su kotu, alƙalai kuwa suka yanke hukunci a kan batun, suka kuɓutar da marar laifi sa’an nan suka hukunta mai laifi,
If there is some legal argument between two people, they are to go to court to have the case judged, in order to justify the one who is right and condemn the one who is wrong.
2 in mai laifin ya cancanci bulala, alƙali zai sa yă kwanta a yi masa bulala a gabansa da yawan bulalan da ya dace da laifin,
If the person who is guilty is sentenced to be flogged, the judge shall order them to lie down and be flogged before him with the number of lashes the crime deserves.
3 amma kada yă yi masa bulala fiye da arba’in. In ya yi masa fiye da haka, za a ƙasƙantar da ɗan’uwanku, zai kuma zama rainanne a idonku.
They are not to receive more than forty lashes. More than that would be to publicly humiliate them.
4 Kada ku yi wa saniya takunkumi sa’ad da take tattaka hatsi.
Don't muzzle an ox when it is treading out the grain.
5 In’yan’uwa suna zama tare, in ɗayansu ya mutu babu ɗa, kada gwauruwar tă yi aure waje da iyalin. Ɗan’uwan mijinta zai ɗauke ta, yă aure ta, yă kuma cika abin da yă kamaci ɗan’uwan miji yă yi.
When two brothers live near to each other and one of them dies without having a son, the widow is not to marry a stranger outside the family. Her husband's brother is to marry her and sleep with her, fulfilling the requirements of a brother-in-law to provide her with children.
6 Ɗan farin da ta haifa zai ɗauki sunan ɗan’uwan da ya rasu saboda kada sunansa yă ɓace daga Isra’ila.
The first son she has will be named after the dead brother, so that his name won't be forgotten in Israel.
7 Amma fa, in mutum ba ya so yă auri matar ɗan’uwansa, sai tă tafi wurin dattawa a ƙofar gari tă ce, “Ɗan’uwan mijina ya ƙi yă wanzar da sunan ɗan’uwansa a Isra’ila. Ya ƙi yă cika abin da ya kamaci ɗan’uwan miji yă yi gare ni.”
However, if the man refuses to marry his brother's widow, she shall go to the elders at the town gate and tell them, “My husband's brother is refusing to keep his brother's name alive in Israel. He doesn't want to perform the requirements of a brother-in-law for me.”
8 Sai dattawan garinsa su kira shi, su kuma yi masa magana. In ya nace yana cewa, “Ba na so in aure ta,”
The town elders are to summon him and talk with him. If he continues to refuse and says, “I don't want to marry her,”
9 sai gwauruwan nan, matar ɗan’uwansa tă haura wurinsa a gaban dattawa, tă tuɓe takalminsa guda, ta tofa masa miyau a fuska, tă ce, “Haka za a yi ga mutumin da zai ƙi kafa gidan ɗan’uwansa.”
his brother's widow is to confront him in the presence of the elders, pull off his sandal, spit in his face, and announce, “This is what happens to the man who refuses to keep his brother's family name alive.”
10 Za a kira zuriyarsa a Isra’ila Iyalin da aka tuɓe masa takalmi.
From then on his family name in Israel will be called “The Family of the Pulled-off Sandal.”
11 In mutane biyu suna faɗa, sai matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don tă kuɓutar da mijinta daga abokin faɗarsa, ta kuma miƙa hannu ta kama marainan wancan,
If two men are fighting, and one of their wives intervenes to save her husband from being beaten, and she grabs hold of the attacker's genitals,
12 sai ku yanke hannunta. Kada ku ji tausayinta.
you are to cut her hand off. Don't show her any mercy.
13 Kada ku kasance da ma’auni iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
Don't have two different measuring weights in your bag, one that's heavy and one that's light.
14 Kada ku kasance da mudu iri biyu a jakarku, ɗaya babba, ɗaya ƙarami.
Don't have two different measuring containers in your house, one that's large and one that's small.
15 Dole ku kasance da ma’aunin da kuma mudun da yake daidai, kuma na gaskiya, saboda ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
Make sure you always use accurate and true weights and measures. In that way you will have long lives in the country the Lord your God is giving you.
16 Gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yi waɗannan abubuwa, da kuma mai rashin gaskiya.
Anyone who doesn't do so and cheats like this offends the Lord your God.
17 Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, sa’ad da kuka fito Masar.
Remember what the Amalekites did to you on your way out of Egypt.
18 Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba.
The came out to confront you when you were tired and weary from your journey, and they attacked all those of you who were lagging behind. They didn't have any respect for God.
19 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutu daga dukan abokan gābanku kewaye da ku, a ƙasar da yake ba ku ku mallaka a matsayin gādo, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta!
Once the Lord your God gives you peace after fighting your enemies in the country that he's giving you to take over and own, you are to wipe out even the memory of the Amalekites from the earth. Don't forget!