< Maimaitawar Shari’a 22 >

1 In kun ga saniya ko tunkiyar ɗan’uwanku wadda ta ɓace, kada ku ƙyale ta, amma ku tabbata kun komar da ita gare shi.
You must not watch your fellow Israelite's ox or his sheep go astray and hide yourself from them; you must surely bring them back to him.
2 In ɗan’uwan ba ya zama kusa da ku, ko kuwa ba ku san shi ba, sai ku kai ta gida ku ajiye ta sai ya zo nemanta. Sa’an nan ku ba shi ita.
If your fellow Israelite is not near to you, or if you do not know him, then you must bring the animal home to your house, and it must be with you until he looks for it, and then you must restore it to him.
3 Ku yi haka in kun sami jakin ɗan’uwanku, ko rigarsa, ko kowane abin da ya ɓace. Kada ku ƙyale shi.
You must do the same with his donkey; you must do the same with his garment; you must do the same with every lost thing of your fellow Israelite's, anything that he has lost and you have found; you must not hide yourself.
4 In kuka ga jakin ɗan’uwanku, ko saniyarsa ya fāɗi a kan hanya, kada ku ƙyale shi. Ku taimaka, ku tā da shi.
You must not see your fellow Israelite's donkey or his ox fallen down in the road and hide yourself from them; you must surely help him to lift it up again.
5 Kada mace ta sa suturar maza, kada kuma namiji ya sa suturar mata, gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamar duk mai yin haka.
A woman must not wear what pertains to a man, and neither must a man put on women's clothing; for whoever does these things is an abomination to Yahweh your God.
6 In kuka ga gidan tsuntsu kusa da hanya, ko a kan itace, ko kuma a ƙasa, mahaifiyar tsuntsun kuwa tana kwance a kan’ya’yanta, ko kuwa a kan ƙwanta, kada ku kama mahaifiyar duk da’ya’yan.
If a bird's nest happens to be in front of you on the road, in any tree or on the ground, with young ones or eggs in it, and the mother sitting on the young or on the eggs, you must not take the mother along with the young.
7 Za ku iya kwashe’ya’yan, amma ku tabbata kun bar mahaifiyar tă tafi. Yin haka zai sa ku sami zaman lafiya da tsawon rai.
You must surely let the mother go, but the young you may take for yourself. Obey this command so that it may go well with you, and that you may prolong your days.
8 Sa’ad da kuka gina sabon gida, ku ja masa dakali kewaye da rufinku don kada ku jawo laifin zub da jini a kan gidanku in wani ya fāɗi daga kan rufin.
When you build a new house, then you must make a railing for your roof so that you do not bring blood on your house if anyone falls from there.
9 Kada ku shuka iri biyu a gonar inabinku; in kuka yi haka, ba abin da kuka shuka ne kaɗai zai ƙazantu ba, amma har da inabinku ma.
You must not plant your vineyard with two kinds of seed, so that the whole harvest is not confiscated by the holy place, the seed that you have sown and the yield of the vineyard.
10 Kada ku haɗa bijimi da jaki su yi noma tare.
You must not plow with an ox and a donkey together.
11 Kada ku sa rigar ulu da aka gauraye da lilin aka saƙa.
You must not wear fabric made of wool and linen together.
12 Ku yi tuntu a kusurwan huɗu na rigar da kuke sa.
You must make yourself fringes on the four corners of the cloak with which you clothe yourself.
13 In mutum ya auri mace, bayan ya kwana da ita, sa’an nan ya ƙi ta
Suppose a man takes a wife, sleeps with her, and then hates her,
14 ya kuma zarge ta, ya ba ta mummunan suna, yana cewa, “Na auri wannan mata, amma sa’ad da na kusace ta, ban sami tabbaci cewa ita budurwa ba ce,”
and then accuses her of shameful things and puts a bad reputation on her, and says, 'I took this woman, but when I came near to her, I found no proof of virginity in her.'
15 sai mahaifin yarinyar da mahaifiyarta su kawo shaida cewa ita budurwa ce wa dattawan gari a ƙofar garin.
Then the father and mother of the girl must take proof of her virginity to the elders at the city gate.
16 Mahaifin yarinyar zai ce wa dattawa, “Na ba da’yata aure ga wannan mutum, amma ya ƙi ta.
The girl's father must say to the elders, 'I gave my daughter to this man as a wife, and he hates her.
17 Yanzu ya zage ta cewa, ‘Ban sami’yarku budurwa ba.’ Amma ga shaidar budurcin’yata.” Sa’an nan iyayenta za su shimfiɗa zanen a gaban dattawan garin,
See, he has accused her of shameful things and said, “I did not find in your daughter the proof of virginity.” But here is the proof of my daughter's virginity.' Then they will spread the garment out before the elders of the city.
18 dattawan kuwa za su ɗauki mutumin su hukunta shi.
The elders of that city must take that man and punish him;
19 Za su ci masa tara shekel azurfa ɗari, su ba mahaifin yarinyar, domin wannan mutum ya ba wa budurwa mutuniyar Isra’ila mummunan suna. Za tă ci gaba da zama matarsa; ba kuwa zai sake ta ba muddin ransa.
and they must fine him one hundred shekels of silver, and give them to the father of the girl, because the man has caused a bad reputation for a virgin of Israel. She must be his wife; he may not send her away during all his days.
20 Amma fa in zarge gaskiya ne, ba a kuwa sami shaidar budurcin yarinyar ba,
But if this thing is true, that the proof of virginity was not found in the girl,
21 sai a kawo ta a ƙofar gidan mahaifinta, a can mazan gari za su jajjefe ta da dutse har tă mutu. Ta yi abin kunya a Isra’ila ta wurin lalaci a yayinda take a gidan mahaifinta. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
then they must bring out the girl to the door of her father's house, and the men of her city must stone her to death with stones, because she has committed a disgraceful action in Israel, to act as a harlot in her father's house; and you will remove the evil from among you.
22 In aka kama wani yana kwance da matar wani, dole a kashe dukansu biyu, wato, mutumin da ya kwana da matar da kuma matar. Dole a fid da mugu daga Isra’ila.
If a man is found sleeping with a woman who is married to another man, then they must both die, the man who was sleeping with the woman and the woman herself; and you will remove the evil from among you.
23 In mutum ya sadu da budurwa a gari wadda aka yi alkawarin aure, ya kuma kwana da ita
If there is a girl who is a virgin, engaged to a man, and another man finds her in the city and sleeps with her,
24 sai ku ɗauki su biyu zuwa ƙofar wannan gari, ku jajjefe su da dutse har su mutum, za a kashe yarinyar domin tana a cikin gari ba ta kuwa yi ihu neman taimako ba, za a kashe mutumin domin ya yi lalata da matar wani. Dole ku fi da mugu daga cikinku.
take both of them to the city gate, and stone them to death. You must stone the girl, because she did not cry out, even though she was in the city. You must stone the man, because he violated his neighbor's wife; and you will remove the evil from among you.
25 Amma in a bayan gari ne mutumin ya sadu da yarinyar da aka yi alkawari aure, ya kuma yi mata fyaɗe, mutumin da ya yi wannan ne kaɗai zai mutu.
But if the man finds the engaged girl in the field, and if he seizes her and sleeps with her, then only the man who sleeps with her must die.
26 Kada ku yi wa yarinyar kome, ba tă yi zunubin da ya cancanci mutuwa ba. Wannan batu ya yi kamar da na mutumin da ya fāɗa wa maƙwabcinsa ya kuma kashe shi.
But to the girl you must do nothing; there is no sin worthy of death in the girl. For this case is like when a man attacks his neighbor and kills him.
27 Tun da ya same ta a jeji ne, wataƙila yarinyar ta yi kukan neman taimako, amma babu wani da zai cece ta.
For he found her in the field; the engaged girl cried out, but there was no one to save her.
28 In mutum ya sadu da yarinyar da ba a yi alkawarin aurenta ba, ya kuma yi mata fyaɗe, aka kuma kama su,
If a man finds a girl who is a virgin but who is not engaged, and if he seizes her and sleeps with her, and if they are discovered,
29 sai yă biya mahaifin yarinyar shekel hamsin na azurfa. Dole yă auri yarinyar, gama ya yi lalata da ita. Ba zai taɓa sake ta ba muddin ransa.
then the man who slept with her must give fifty shekels of silver to the girl's father, and she must become his wife, because he has humiliated her. He may not send her away during all his days.
30 Kada mutum yă auri matar mahaifinsa, kada yă ƙasƙantar gādon mahaifinsa.
A man must not take his father's wife as his own; he must not take away his father's marriage rights.

< Maimaitawar Shari’a 22 >