< Maimaitawar Shari’a 19 >

1 Sa’ad da Ubangiji Allahnku ya hallakar da al’ummai waɗanda yake ba ku ƙasarsu, sa’ad da kuka kore su, kuka kuma zauna a birane da gidajensu,
After the Lord your God has destroyed the nations whose land he's giving you, and after you have driven them out and settled in their cities and houses,
2 sai ku keɓe wa kanku birane uku waɗanda suke a tsakiyar ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka.
then you are to choose three sanctuary towns in the country that the Lord your God is giving you to own.
3 Ku gina hanyoyi zuwa cikinsu, ku kuma raba ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo kashi uku, saboda duk wani da ya yi kisankai yă iya gudu zuwa can.
You are build roads to these towns. Divide the country the Lord is giving you into three sections. This way anyone who kills someone else can easily run to these towns for protection.
4 Ga doka game da mutumin da ya kashe wani, ya kuma gudu don yă cece ransa, wani wanda ya kashe maƙwabcinsa ba da gangan ba, ba kuwa da wata ƙiyayya a tsakaninsu a dā ba.
This is what is to happen when a person accidentally kills someone else without meaning to, and runs to one of these sanctuary towns to save their life.
5 Misali, in mutum ya je jeji da maƙwabcinsa domin yankan itace, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe daga ƙotar yayinda yake saran itacen, ya sari maƙwabcin har ya mutu. Mutumin nan zai iya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane don yă ceci ransa.
For example, if a man goes to cut wood in the forest with his friend and swings his axe to chop down a tree, but the head flies off the handle and hits and kills his friend, he may run to one of these towns to save his life.
6 In ba haka ba mai neman ɗaukan fansa jini, zai iya binsa cikin fushi, yă cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā.
Otherwise the avenger in his anger might chase after the man and catch up with him and kill him, if it's a long distance. The man would be killed even though he didn't deserve to die, because he hadn't meant to cause any harm.
7 Wannan ne ya sa na umarce ku ku keɓe wa kanku birane uku.
This is the reason why I'm giving this order to choose three sanctuary towns.
8 In Ubangiji Allahnku ya fadada yankinku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa wa kakanninku, ya kuma ba ku ƙasar gaba ɗaya kamar yadda ya yi musu alkawari,
Should the Lord your God expand your territory, as he promised your forefathers, and give you all the land he said he would,
9 idan dai kun lura, kuka kiyaye umarnin da nake ba ku a yau, wato, ta wurin ƙaunar Ubangiji Allahnku, kuka kuma yi tafiya kullum cikin hanyoyinsa, to, sai ku keɓe ƙarin birane uku.
and if you are careful to keep all these commandments I'm giving you today, loving the Lord your God and always following his ways, then you are to choose three additional three sanctuary towns.
10 Ku yi haka don kada a zub da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, don kada ku kuma zama masu laifin zub da jini.
In this way the blood of innocent people won't not be shed in the country the Lord your God is giving you to own and you won't be responsible for the death of innocent people who aren't guilty of losing their lives.
11 Amma idan wani mutum yana ƙin maƙwabcinsa, ya kuma yi kwanto yana fakonsa, ya yi masa rauni, har ya kashe shi, sa’an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin waɗannan birane,
On the other hand, if a man hates someone, hides in wait, and attacks and kills them, and then the killer runs to one of the sanctuary towns,
12 dattawan garinsa za su aika a kawo shi, a dawo da shi daga birnin, a miƙa shi ga mai neman fansar jini don yă kashe shi.
the elders of his home town must send for him, bring him back, and hand him over to the avenger to be killed.
13 Kada ku ji tausayinsa. Dole ku fid da laifin zub da jinin marar laifi daga Isra’ila, don ku sami zaman lafiya.
Show him no mercy. You are to eliminate from Israel the guilt of shedding the blood of the innocent, and then all will be well.
14 Kada ka gusar da dutsen nuna shaidar iyakar maƙwabcinka wanda kakanni suka sa, a gādon da ka samu a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka mallaka.
Don't move your neighbor's boundary marker. It was placed there by your ancestors to mark the land allotment you will receive in the country that the Lord your God is giving you to own.
15 Shaidar mutum guda ba tă isa a tabbatar cewa mutum yana da laifi game da laifin da ake tuhumarsa ba, ko kuwa a kan wani laifin da ake zaginsa da aikata ba. Dole a tabbata da batun ta bakin shaidu biyu, ko uku.
The evidence given by a single witness is not enough to prove a sin or a crime against someone, never mind what offense they are alleged to have committed. The facts must be confirmed by the evidence given by two or three witnesses.
16 In wani ɗan sharri ya tashi ya yi wa wani sharri, don a sami wani da laifi,
If someone falsely accuses another person of a crime,
17 dole mutanen nan biyu da suke rikici su tsaya a gaban Ubangiji, a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin.
both those involved must come to be judged in the presence of the Lord by the priests and judges who are then in office.
18 Dole alƙalan su yi bincike sosai, in kuma aka tabbatar mai ba da shaida maƙaryaci ne, yana ba da shaidar zur a kan ɗan’uwansa ne,
The judges shall conduct a full investigation, and if the accuser proves to be a liar who has made false accusations
19 to, sai a yi da shi yadda ya yi niyya yă yi da ɗan’uwansa. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
then you must punish the accuser in the same way they wanted to punish their victim. You must eliminate this evil from among you.
20 Sauran mutane za su ji wannan su kuma ji tsoro, ba kuwa za a ƙara yin irin wannan mugun abu a cikinku ba.
Then the rest of the people will hear and be afraid, and they will never again do anything so evil among you. Then everyone else will hear about it and be afraid, and won't ever do anything so evil.
21 Kada ku ji tausayi, rai yă zama a maimakon rai, ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa.
Don't show any mercy. The rule is life for life, eye for eye, tooth for tooth, hand for hand, and foot for foot.

< Maimaitawar Shari’a 19 >