< Maimaitawar Shari’a 17 >
1 Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku, saniya ko tunkiyar da take da wani lahani, ko naƙasa a cikinta, gama wannan zai zama abar ƙyama gare shi.
Don't sacrifice to the Lord your God cattle or a sheep that has a defect or has something seriously wrong, for that is offensive to the Lord your God.
2 In an sami wani namiji ko ta mace mai zama a cikinku, a ɗaya daga biranen da Ubangiji ya ba ku yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku ta wurin karya alkawarinsa,
There may be a report that one of you, whether a man or a woman, living in a town that the Lord your God gave you, has been found to be sinning in the sight of the Lord your God by breaking the Lord's agreement.
3 wanda ya saba wa umarnina, har ya yi sujada ga waɗansu alloli, yana rusuna musu, ko ga rana, ko ga wata, ko kuwa ga taurarin sama,
This person has done this by going to worship other gods, bowing down to them—or to the sun, moon, or any of the stars of heaven—which I have ordered you not to do.
4 in kuwa aka faɗa muku wannan, to, dole a bincika sosai. In kuwa gaskiya ne, aka kuma tabbatar cewa wannan abin ƙyama ya faru a cikin Isra’ila,
If you hear such a report, you need to make a full investigation. If you find out that the report is true, and that such an awful sin has been committed in Israel,
5 sai a ɗauki namijin, ko ta mace wanda ya aikata wannan mugun abu zuwa ƙofar birni, a jajjefe wannan mutum sai ya mutu.
you must have the man or woman who has committed this terrible act taken outside the town and stoned to death.
6 Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku, za a iya kashe mutum, amma ba za a iya kashe mutum bisa ga shaida mutum guda ba.
That person is to be executed based on the evidence given by two or three witnesses. No one shall be executed on the evidence given by a single witness.
7 Hannuwan shaidun ne za su zama na farko a kisan wanda ake zargin, sa’an nan hannuwan dukan mutane. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
The witnesses must act first in executing the person, and then the rest of those who are present. You must eliminate the evil from among you.
8 In aka kawo ƙarar da yake da wuya sosai ga alƙali a kotunanku, ko wadda aka zub da jini ne, ko ta faɗa ce, ko kuwa ta wadda aka ci mutunci ce, ku kai su wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa.
If there's a case before your town court that is too problematic for you to settle, whether the argument is over murder or manslaughter, one legal decision against another, or different degrees of assault, you must take the issue to the place the Lord your God will choose.
9 Ku je wurin firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, ga kuma alƙalin wanda yake mulki a lokacin. Ku bincika daga gare su, za su kuwa ba da hukunci.
Go to the priests, the Levites, and to the judge in charge. Present the case to them, and they will give you their decision.
10 Dole ku aikata hukuncin da suka yi a wurin da Ubangiji zai zaɓa. Ku lura fa, ku aikata kome da suka faɗa muku.
You must abide by the decision they give you there at the place the Lord will choose. Make sure you do everything they tell you to do,
11 Ku yi bisa ga dokar da suka koyar muku da kuma hukuncin da suka yi muku. Kada ku juya daga abin da suka faɗa muku, ko zuwa dama, ko zuwa hagu.
in accordance with the legal instructions they give you and the verdict they delivered. Don't deviate from the decision they give you.
12 Duk mutumin da ya yi rashin hankali wa alƙali, ko ga firist wanda yake aiki a nan wa Ubangiji Allahnku, dole a kashe shi. Dole ku fid da mugu daga Isra’ila.
Anyone who treats with contempt either the priest (who ministers before the Lord your God) or the judge, must be executed. You must eliminate this evil from Israel.
13 Dukan mutane kuwa za su ji, su kuma ji tsoro, ba kuwa za su ƙara yin rashin hankali kuma ba.
Then everyone else will hear about it and be afraid, and won't act with contempt in the future.
14 Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kuka mallake ta, kuka kuma zauna a cikinta, sai kuka ce, “Bari mu naɗa sarki a kanmu kamar sauran al’umman da suke kewaye da mu,”
After you've entered the land that the Lord your God is giving you, and have taken it over and settled in it, and you decide, “Let's have a king to rule over us like all the other nations around us do,”
15 ku tabbata kun naɗa sarki a kanku wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa ne. Dole yă zama daga cikin’yan’uwanku. Kada ku sa baƙo a kanku, wanda ba mutumin Isra’ila ɗan’uwanku ba.
you can have a king but only one chosen by the Lord your God. He must be an Israelite. You must not have a king who is a foreigner; someone who is not an Israelite.
16 Sarkin, ba zai nemi dawakai da yawa wa kansa ba, ko yă sa mutane su koma Masar don su sami ƙarin dawakai ba, gama Ubangiji ya faɗa muku, “Ba za ku ƙara koma wancan hanya kuma ba.”
Your king must not have large numbers of horses, or send his men to Egypt to buy more horses, because the Lord has declared, “You must never to return there again.”
17 Sarkin ba zai auri mata masu yawa ba, in ba haka ba zuciyarsa za tă karkata. Ba zai tara azurfa da zinariya da yawa ba.
He must not have many wives, so they don't lead him away from following the Lord. He must not have large quantities of silver and gold.
18 Sa’ad da ya hau kursiyin mulkinsa, sai yă rubuta wa kansa a littafin kofin wannan doka da aka ɗauka daga na firistoci, waɗanda suke Lawiyawa.
Once he is king and sits on his royal throne, he must make a copy for himself of these instructions, writing them on a scroll in the presence of the Levitical priests.
19 Zai kasance tare da shi, zai kuma karanta shi dukan kwanakin ransa, saboda yă koyi girmama Ubangiji Allahnsa, yă kuma bi dukan kalmomin wannan doka da kuma waɗannan ƙa’idodi a hankali
He is to keep it with him, and he is to read from it each day throughout his life, so he may learn to respect the Lord his God by being careful to follow every word of these instructions and regulations.
20 don kada yă ɗauki kansa ya fi’yan’uwansa, yă kuma juya daga dokar zuwa dama, ko zuwa hagu. Sa’an nan shi da kuma zuriyarsa za su daɗe suna mulki a Isra’ila.
Then he won't think more of himself than his fellow Israelites, and he won't deviate from the commandments, so that he and his sons may have long reigns over the kingdom of Israel.