< Maimaitawar Shari’a 13 >

1 In wani annabi ko mai mafarkai, ya bayyana a cikinku, ya kuma yi muku shelar wata alama mai banmamaki ko al’ajabi,
“When a prophet or a dreamer of a dream arises in your midst, and he has given a sign or wonder to you,
2 in kuwa alamar, ko al’ajabin da annabin ya yi faɗin ya faru, ya kuma ce, “Bari mu bi waɗansu alloli (allolin da ba ku sani ba) mu kuma yi musu sujada,”
and the sign and the wonder has come to pass, which he has spoken of to you, saying, Let us go after other gods (which you have not known) and serve them,
3 kada ku saurari kalmomin wannan annabi ko mai mafarki. Ubangiji Allahnku yana gwada ku ne don yă sani ko kuna ƙaunarsa da dukan zuciyarku da kuma dukan ranku.
you do not listen to the words of that prophet or to that dreamer of the dream, for your God YHWH is trying you to know whether you are loving your God YHWH with all your heart and with all your soul;
4 Ubangiji Allahnku ne za ku bi, shi ne kuma za ku girmama. Ku kiyaye umarnansa, ku kuma yi masa biyayya; ku bauta masa, ku kuma manne masa.
you walk after your God YHWH, and you fear Him, and you keep His commands, and you listen to His voice, and you serve Him, and you cleave to Him.
5 Dole a kashe wannan annabi ko mai mafarki, domin ya yi wa’azin tawaye ga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, ya fanshe ku daga ƙasar bauta; gama annabin nan ya yi ƙoƙari yă juye daga hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, ku bi. Dole ku fid da mugu daga cikinku.
And that prophet or that dreamer of the dream is put to death, for he has spoken apostasy against your God YHWH (who is bringing you out of the land of Egypt, and has ransomed you out of a house of servants), to drive you out of the way in which your God YHWH has commanded you to walk, and you have put away evil from your midst.
6 In ɗan’uwanka, ko ɗanka, ko’yarka, ko matar da kake ƙauna, ko abokinka na kusa, a ɓoye ya ruɗe ka, yana cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ko kai, ko kakanninka ba su sani ba,
When your brother, son of your mother, or your son, or your daughter, or the wife of your bosom, or your friend who [is] as your own soul, moves you in secret, saying, Let us go and serve other gods (which you have not known, you and your fathers,
7 allolin mutanen kewayenku, ko na kusa, ko na nisa, daga wannan ƙarshen ƙasar zuwa wancan),
of the gods of the peoples who [are] around you, who are near to you, or who are far off from you, from the end of the earth even to the [other] end of the earth),
8 kada ka yarda da shi, kada ma ka saurare shi. Kada ka ji tausayinsa. Kada ka haƙura da shi, ko ka tsare shi.
you do not consent to him, nor listen to him, nor does your eye have pity on him, nor do you spare, nor do you cover him over.
9 Dole ka kashe shi. Dole hannunka yă zama na farko a kisansa, sa’an nan hannuwan sauran dukan mutane.
But you surely kill him; your hand is on him in the first place to put him to death, and the hand of all the people last;
10 Ku jajjefe shi da duwatsu har sai ya mutu, domin ya yi ƙoƙari yă juye ku daga Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar, daga ƙasar bauta kuma.
and you have stoned him with stones and he has died, for he has sought to drive you away from your God YHWH, who is bringing you out of the land of Egypt, out of a house of servants;
11 Sa’an nan dukan Isra’ila za su ji su kuma tsorata, babu kuma wani a cikinku da zai ƙara yin irin wannan mugun abu.
and all Israel hears and fears, and does not add to do like this evil thing in your midst.
12 In kuka ji an yi magana a kan wani daga cikin biranen da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku zauna a ciki
When you hear [someone] in one of your cities, which your God YHWH is giving to you to dwell there, saying,
13 cewa mugaye sun taso a cikinku, suna rikitar da mutane a birni, suna cewa, “Mu je mu yi wa waɗansu alloli sujada” (allolin da ba ku sani ba),
Men, sons of worthlessness, have gone out of your midst, and they force away the inhabitants of their city, saying, Let us go and serve other gods (which you have not known),
14 to, sai ku bincike labarin sosai a hankali. In kuwa gaskiya ne, an kuma tabbatar wannan abin ƙyama ya faru a cikinku,
then you have inquired, and searched, and asked diligently, and behold, [if] truth, the thing is established; this abomination has been done in your midst—
15 dole a karkashe dukan waɗanda suke zama a wannan birni da takobi. Ku hallaka su ƙaƙaf, ku karkashe mutanen birnin da kuma dabbobinsa.
you surely strike the inhabitants of that city by the mouth of the sword, devoting it and all that [is] in it, even its livestock, by the mouth of the sword.
16 Ku tattara dukan ganimar birnin a tsakiyar gari, ku ƙone birnin da kuma ganimar ƙurmus a matsayin hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. Birnin zai kasance kufai har abada, kada a sāke gina shi.
And you gather all its spoil into the midst of its broad place, and have completely burned the city and all its spoil with fire for your God YHWH, and it has been a continuous heap, it is not built anymore;
17 Ba za a iske wani daga cikin abubuwan nan da aka haramta a hannuwanku ba, saboda Ubangiji yă juya daga fushinsa mai ƙuna, yă nuna jinƙai, yă ji tausayinku, yă kuma ƙara yawanku, kamar yadda ya alkawarta da rantsuwa ga kakanninku,
and nothing from any of that [which is] devoted stays in your hand, so that YHWH turns back from the fierceness of His anger, and has given mercies to you, and loved you, and multiplied you, as He has sworn to your fathers,
18 domin kun yi biyayya da Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye dukan umarnan da nake ba ku a yau, kuna kuma aikata abin da yake daidai a idanunsa.
because you listen to the voice of your God YHWH, to keep all his commands which I am commanding you today, to do that which [is] right in the eyes of your God YHWH.”

< Maimaitawar Shari’a 13 >