< Maimaitawar Shari’a 1 >

1 Waɗannan su ne kalmomin da Musa ya yi wa dukan Isra’ila, a hamada gabas da Urdun, wato, Araba, ɗaura da Suf, tsakanin Faran da Tofel, Laban, Hazerot da Dizahab.
Şeria Irmağı'nın doğu yakasındaki çölde, Suf'un karşısında Arava'da, Paran ile Tofel, Lavan, Haserot, Di-Zahav arasında Musa İsrailliler'e şunları anlattı.
2 (Yakan ɗauki kwana goma sha ɗaya daga Horeb zuwa Kadesh Barneya ta hanyar Dutsen Seyir.)
Horev'den Seir Dağı yoluyla Kadeş-Barnea'ya gitmek on bir gün sürer.
3 A shekara ta arba’in, a rana ta fari ga wata na goma sha ɗaya, Musa ya yi shela ga Isra’ilawa game da dukan abin da Ubangiji ya umarta shi game da su.
Mısır'dan çıktıktan sonra kırkıncı yılın on birinci ayının birinci günü, Musa RAB'bin, kendisi aracılığıyla İsrailliler'e neler buyurduğunu anlattı.
4 Wannan ya faru bayan ya ci Sihon sarkin Amoriyawa wanda ya yi mulki a Heshbon da yaƙi. A Edireyi kuma ya ci Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot da yaƙi.
Bu olay Musa Heşbon'da yaşayan Amorlular'ın Kralı Sihon'u, Aştarot'ta ve Edrei'de yaşayan Başan Kralı Og'u bozguna uğrattıktan sonra oldu.
5 Gabas da iyakar Mowab, Musa ya fara bayyana wannan doka, yana cewa,
Musa Şeria Irmağı'nın doğu yakasındaki Moav topraklarında bu yasayı şöyle açıklamaya başladı:
6 Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb cewa, “Daɗewarku a wannan dutse ya isa haka.
“Tanrımız RAB Horev'de bize, ‘Bu dağda yeteri kadar kaldınız’ dedi,
7 Ku tashi, ku ci gaba zuwa ƙasar tudun Amoriyawa; ku tafi wurin dukan maƙwabta a cikin Araba, a cikin duwatsu, a gindin yammancin tuddai, a Negeb da kuma a ta kwaruruka, da ƙasar Kan’aniyawa da kuma zuwa Lebanon, har zuwa babban kogi, wato, Yuferites.
‘Haydi kalkın, Arava'da, dağlık bölgede, Şefela'da, Negev'de ve Akdeniz kıyısında yaşayan bütün komşu halklara, Amorlular'ın dağlık bölgesine, büyük Fırat Irmağı'na kadar uzanan Kenanlılar ülkesine ve Lübnan'a gidin.
8 Duba na riga na ba ku wannan ƙasa. Ku shiga ku mallaki ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba wa kakanninku, ga Ibrahim, Ishaku da kuma Yaƙub, da kuma ga zuriyarsu bayansu.”
Bu toprakları size verdim. Gidin, atalarınıza, İbrahim'e, İshak'a, Yakup'a ve soylarına ant içerek söz verdiğim toprakları mülk edinin.’”
9 A wancan lokaci na faɗa muku cewa, “Ku kaya ne masu nauyi da ni kaɗai ba zan iya ɗauka ba.
“O sırada size, ‘Tek başıma yükünüzü taşıyamam’ dedim,
10 Ubangiji Allahnku ya ƙara yawanku har yau kuka zama da yawa kamar taurari a sarari.
‘Tanrınız RAB sizi çoğalttı. Bugün göklerdeki yıldızlar kadar çoğaldınız.
11 Bari Ubangiji, Allahn kakanninku yă ƙara yawanku sau dubu, yă kuma albarkace ku yadda ya yi alkawari!
Atalarınızın Tanrısı RAB sizi bin kat daha çoğaltsın ve söz verdiği gibi kutsasın!
12 Amma yaya zan ɗauka dukan damuwoyinku da nawayarku da kuma faɗace-faɗacenku duka ni kaɗai?
Sorunlarınıza, yükünüze, davalarınıza ben tek başıma nasıl katlanabilirim?
13 Ku zaɓi waɗansu masu hikima, masu ganewa, da kuma mutanen da ake girmama daga kowace kabilarku, zan kuma sa su a kanku.”
Kendinize her oymaktan bilge, anlayışlı, deneyimli adamlar seçin. Onları size önder atayacağım.’
14 Kuka amsa mini, kuka ce, “Abin da ka ce za ka yi, yana da kyau.”
“Siz de bunun iyi olduğunu onayladınız.
15 Saboda haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma’amala da jama’a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu-dubu, waɗansu a kan ɗari-ɗari, waɗansu a kan hamsin-hamsin, waɗansu kuma a kan goma-goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku.
Böylece oymaklarınızın bilge ve deneyimli kişiler olan ileri gelenlerini size önder atadım. Onlara biner, yüzer, ellişer, onar kişilik toplulukların sorumluluğunu verdim. Oymaklarınız için de yöneticiler görevlendirdim.
16 Na kuma umarci alƙalanku a wancan lokaci, na ce, “Ku yi adalci cikin shari’a tsakanin’yan’uwanku, ko damuwar tana tsakanin’yan’uwa Isra’ilawa ne, ko kuwa tsakanin Isra’ilawa da baƙin da suke zaune a cikinku.
Ayrıca yargıçlarınıza, ‘Kardeşleriniz arasındaki sorunları dinleyin’ dedim, ‘Bir adamla İsrailli kardeşi ya da bir yabancı arasındaki davalarda adaletle karar verin.
17 Kada ku nuna sonkai a cikin hukuncinku, ku saurari kowane ɓangare, babba da ƙarami, kada ku ji tsoron wani, gama hukunci na Allah ne. Ku kawo kowane batun da ya sha ƙarfinku, zan kuwa saurare shi.”
Yargılarken kimseyi kayırmayın; küçüğe de, büyüğe de aynı gözle bakın. Hiç kimseden korkmayın. Yargı Tanrı'ya özgüdür. Çözemeyeceğiniz bir sorun olursa bana getirin, ben gerekeni yaparım.’
18 A wancan lokacin kuwa na faɗa muku dukan abin da ya kamata ku yi.
O sırada yapmanız gereken her şeyi size buyurmuştum.”
19 Sa’an nan, muka kama hanya daga Horeb muka ratsa wajen ƙasar tudun Amoriyawa ta dukan hamadarta mai fāɗi, da kuma mai bantsoron da kuka gani, muka kuma kai Kadesh Barneya yadda Ubangiji, Allahnmu ya umarce mu.
“Sonra Tanrımız RAB'bin bize buyurduğu gibi Horev'den ayrıldık, Amorlular'ın dağlık bölgesine giden yoldan geçerek gördüğünüz o geniş ve korkunç çölü aşıp Kadeş-Barnea'ya vardık.
20 Sai na ce muku, “Kun iso ƙasar tudun Amoriyawa, wadda Ubangiji, Allahnmu yake ba mu.
Size, ‘Tanrımız RAB'bin bize vereceği Amorlular'ın dağlık bölgesine vardınız’ dedim,
21 Duba, Ubangiji Allahnku ya ba ku ƙasar. Ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allahn kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro, kada ku fid da zuciya.”
‘İşte, Tanrınız RAB size ülkeyi verdi. Haydi, atalarınızın Tanrısı RAB'bin size söylediği gibi, gidip orayı mülk edinin. Korkmayın, yılmayın.’
22 Sai dukanku kuka zo wurina kuka ce, “Bari mu aiki mutane su yi gaba su leƙi mana asirin ƙasar, su kuma kawo mana labari game da hanyar da za mu bi, da kuma biranen da za mu shiga.”
“O zaman hepiniz bana gelip, ‘Ülkeyi araştırmak için önümüzden adamlar gönderelim’ dediniz, ‘Hangi yoldan gideceğiz, hangi kentlere uğrayacağız? Bilgi versinler.’
23 Ra’ayin nan naku ya yi mini kyau, saboda haka na zaɓe ku goma sha biyu, mutum guda daga kowace kabila.
“Bu düşünceyi benimsedim. Her oymaktan birer kişi olmak üzere aranızdan on iki kişi seçtim.
24 Suka tafi, suka haura zuwa ƙasar tudu, suka kai Kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar.
Bunlar dağlık bölgeye çıkarak Eşkol Vadisi'ne varıp ülkeyi araştırdılar.
25 Suka ɗebi’ya’yan itatuwan ƙasar, suka sauko mana da su, suka kuma ba da labari cewa, “Ƙasar da Ubangiji Allahnmu yake ba mu, kyakkyawa ce.”
Dönüşte orada yetişen meyvelerden getirdiler ve, ‘Tanrımız RAB'bin bize vereceği ülke verimlidir’ diye haber verdiler.
26 Amma ba ku yi niyya ku haura ba, kuka yi tawaye gāba da umarnin Ubangiji Allahnku.
“Ne var ki, siz oraya gitmek istemediniz. Tanrınız RAB'bin buyruğuna karşı geldiniz.
27 Kuka yi gunaguni a cikin tentunanku, kuna cewa, “Ubangiji ya ƙi mu; shi ya sa ya fitar da mu daga Masar don yă ba da mu ga hannuwan Amoriyawa su hallaka mu.
Çadırlarınızda söylenerek, ‘RAB bizden nefret ediyor’ dediniz, ‘Bizi Amorlular'ın eline verip yok etmek için Mısır'dan çıkardı.
28 Ina za mu?’Yan’uwanmu suka sa muka fid da zuciya. Suka ce, ‘Mutanen sun fi mu ƙarfi, sun kuma fi mu tsayi; biranen manya ne, da katanga har sama. Mun ma ga Anakawa a can.’”
Oraya niye gidelim? Kardeşlerimiz yöre halkının bizden daha güçlü, daha uzun boylu olduğunu söyleyerek cesaretimizi kırdılar. Kentler büyükmüş, göğe dek yükselen surlarla çevriliymiş. Orada Anaklılar'ı da görmüşler.’
29 Sai na ce muku, “Kada ku firgita; kada ku ji tsoronsu.
“Oysa ben size, ‘Onlardan korkmayın, yılmayın’ dedim,
30 Ubangiji Allahnku yana a gabanku, zai yi yaƙi saboda ku, kamar yadda ya yi a kan idanunku a Masar,
‘Önünüzden giden Tanrınız RAB sizin için savaşacak. Gözünüzün önünde Mısır'da ve çölde sizler için yaptıklarının aynısını yapacak. Tanrınız RAB'bin buraya varıncaya dek, çocuğunu taşıyan bir adam gibi sizi nasıl yol boyunca taşıdığını gördünüz.’
31 da kuma a cikin hamada. A can ma kun ga yadda Ubangiji Allahnku ya riƙe ku ko’ina da kuka tafi, kamar yadda mahaifi yakan riƙe ɗansa, sai da kuka kai wannan wuri.”
32 Duk da haka, ba ku amince da Ubangiji Allahnku ba,
Bütün bunlara karşın Tanrınız RAB'be güvenmediniz.
33 shi da ya sha gabanku a tafiyarku, cikin wuta da dad dare da kuma girgije da rana, don yă nemi wurare domin ku kafa sansani, don kuma yă nuna muku hanyar da za ku bi.
O RAB ki, çadırlarınızı kurmanız için size yer aramak, gideceğiniz yolu göstermek için geceleyin ateşte, gündüzün bulutta önünüzsıra gitti.”
34 Da Ubangiji ya ji abin da kuka faɗa, sai ya husata, ya kuma yi rantsuwa ya ce,
“RAB yakınmalarınızı duyunca öfkelendi ve şöyle ant içti:
35 “Babu wani a cikin wannan muguwar tsara da zai ga ƙasa mai kyau da na rantse zan ba wa kakanninku,
‘Atalarınıza ant içerek söz verdiğim o verimli ülkeyi, bu kötü kuşaktan Yefunne oğlu Kalev dışında hiç kimse görmeyecek. Yalnız o görecek, ayak bastığı toprakları ona ve soyuna vereceğim. Çünkü o bütün yüreğiyle RAB'bin yolunda yürüdü.’
36 sai dai Kaleb ɗan Yefunne. Zai gan ta, zan ba shi duk ƙasar da tafin ƙafarsa ta taka, shi da zuriyarsa, gama ya bi Ubangiji da zuciya ɗaya.”
37 Saboda ku Ubangiji ya husata da ni, ya kuma ce, “Kai ma, ba za ka shiga ƙasar ba.
“Sizin yüzünüzden RAB bana da öfkelenerek, ‘Sen de o ülkeye girmeyeceksin’ dedi,
38 Amma mataimakinka, Yoshuwa ɗan Nun, zai shiga. Ka ƙarfafa shi gama shi ne zai jagoranci Isra’ila su gāje ta.
‘Ama yardımcın Nun oğlu Yeşu oraya girecek. Onu yüreklendir. İsrailliler'in ülkeyi mülk edinmesini o sağlayacak.
39 Amma’ya’yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su za su shiga ƙasar. Zan ba da ita gare su, za su kuwa mallake ta.
Tutsak olacak dediğiniz küçükleriniz, bugün iyiyle kötüyü ayırt edemeyen çocuklarınız oraya girecekler. Ülkeyi onlara vereceğim, orayı onlar mülk edinecekler.
40 Amma ku kam, sai ku juya, ku koma cikin hamada ta hanyar Jan Teku.”
Ama siz geri dönün, Kamış Denizi yolundan çöle gidin.’”
41 Sai kuka amsa, kuka ce, “Mun yi zunubi ga Ubangiji. Za mu haura mu yi yaƙi yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu.” Saboda haka kowannenku ya yi ɗamara da kayan yaƙinsa, kuka yi tsammani zai zama muku da sauƙi ku ci ƙasar tuddai da yaƙi.
“Bunun üzerine bana, ‘RAB'be karşı günah işledik’ dediniz, ‘Tanrımız RAB'bin buyruğu uyarınca gidip savaşacağız.’ Sonra dağlık bölgede savaşmanın kolay olacağını düşünerek her biriniz silahınızı kuşandınız.
42 Amma Ubangiji ya ce mini, “In faɗa muku, ‘Kada ku fāɗa musu da yaƙi, gama ba zai kasance tare da ku ba. Idan kuka kuskura, abokan gābanku za su murƙushe ku.’”
“Ama RAB bana şöyle dedi: ‘Söyle onlara, savaşa gitmesinler. Çünkü sizinle olmayacağım. Düşmanlarınızın önünde yenilgiye uğrayacaksınız.’
43 Sai na faɗa muku, amma ba ku saurara ba. Kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji, a cikin jahilcinku kuwa kuka taka, kuka haura cikin ƙasar tudu.
“Sizi uyardım, ama dinlemediniz. RAB'bin buyruğuna karşı geldiniz. Kendinize güvenerek dağlık bölgeye çıktınız.
44 Amoriyawan da suke zama a waɗannan tuddai, suka fito kamar tarin ƙudan zuma gāba da ku, suka kore ku, suka fatattake ku daga Seyir har zuwa Horma.
Dağlık bölgede yaşayan Amorlular size karşı çıktılar. Arılar gibi sizi kovaladılar. Seir'den Horma Kenti'ne dek sizi bozguna uğrattılar.
45 Kuka dawo, kuka yi kuka a gaban Ubangiji, amma bai kula da ku ba, balle yă saurare ku.
Geri döndünüz ve RAB'bin önünde ağladınız. Ama RAB ne ağlayışınızı duydu, ne de size kulak astı.
46 Haka kuwa kuka zauna a Kadesh kwanaki masu yawa, kuka ci lokaci a can.
Uzun süre Kadeş'te kaldınız.”

< Maimaitawar Shari’a 1 >