< Daniyel 7 >

1 A shekara ta fari ta mulkin Belshazar sarkin Babilon, Daniyel ya yi mafarki, wahayoyi kuma suka ratsa tunaninsa a sa’ad da yake a kwance a gadonsa. Sai ya rubuta abin da mafarkin ya ƙunsa.
In yac se meet ke Belshazzar el tokosra lun acn Babylonia, nga tuh oru mweme se, ac liye sie aruruma ke fong sac. Nga tuh simusla koanon mweme sac, ac pa inge ma nga simusla ke
2 Daniyel ya ce, “A cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga kusurwoyi huɗu na sama suna gurɓata babban teku.
ma nga liye in fong sac: Eng uh tuhtuh yen nukewa me, ac oru meoa uh in arulana pulkulakyak.
3 Sai ga dabbobi huɗu, kowannensu ya yi dabam da sauran, suna fitowa daga teku.
Kosro na lulap sulallal akosr otyak in meoa uh me, ac tia oana sie lumahlos.
4 “Na farkon ya yi kamar zaki kuma yana da fikafikai kamar gaggafa. Ina kallo, sai aka fizge fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum.
Ma soko oemeet ah oana luman lion soko, tusruktu oasr posohksok kacl oana eagle se. Ke nga srakna ngetang liye, na posohksok kacl uh kipatla. Na kosro soko ah touyak ac tulokyak in tu oana mwet se. Itukyang nu sel elan nunak in mwet.
5 “A gabana kuma ga dabba ta biyu, wadda ta yi kamar beyar. Aka ɗaga ta a gefenta guda, tana kuwa da haƙarƙarai uku a bakinta a tsakanin haƙoranta. Aka faɗa mata, ‘Tashi ki cika cikinki da ɗanyen nama!’
Kosro soko aklukwa ah lumahl oana bear soko ma tuyak fin nial tok. El ngalis sri in pap tolkwe ke oalul, ac pusra se fahk nu sel, “Kangla nufon ikwa ma kom ku in kang an!”
6 “Bayan haka, na duba, a gabana kuwa ga wata dabba wadda ta yi kamar Damisa, a bayanta kuma tana da fikafikai huɗu irin na tsuntsu. Wannan dabbar tana da kawuna huɗu, aka kuma ba ta iko tă yi mulki.
Ke nga srakna tu liye, na soko pacna kosro lulap sikyak. Lumahl oana kosro leopard soko, tusruk oasr posohksok akosr oan fintokol, oana posohksok ke won uh, ac oasr sifa akosr kacl. Lumahl oana in oasr wal na fulat lal.
7 “Bayan haka, a cikin wahayina da dare na duba, a gabana kuwa ga dabba ta huɗu, wadda take da bantsoro da banrazana da kuma iko ƙwarai. Tana da manyan haƙoran ƙarfe; ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta. Ta bambanta da dukan sauran dabbobin da suka riga ta, tana kuma da ƙahoni goma.
Ke nga srakna tu liye, kosro lulap soko akakosr ah sikyak. El arulana fokoko, koluk lumahl ac aksangeng ngetngetal. El ac sang wihs osra na lulap kacl uh ac itungya ma el ac sruokya uh, na el ac lolongya in mokutkuti. El tia oana kosro saya uh, mweyen oasr koac singoul kacl.
8 “Yayinda nake cikin tunani game da ƙahonin nan, a gabana kuwa ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙani, wanda ya fito daga cikinsu; kuma an tumɓuke uku daga cikin ƙahonin farko kafin wannan. Wannan ƙaho yana da idanu kamar na mutum da kuma bakin da yake maganganun fariya.
Ke nga ngetang liye koac inge, nga liye koac srisrik soko kapak inmasrlo. El sinukunla tolkwe sin koac ma oan meet ah. Koac srisrik soko inge oasr atronmutun mwet kac, ac sie oalu su arulana yokla tungak la.
9 “Ina cikin dubawa, “sai aka ajiye kursiyoyi, sai ga wani wanda yake tun fil azal ya zauna a mazauninsa. Rigarsa ta yi fari fat kamar ƙanƙara; gashin kansa sun yi fari kamar ulu. Kursiyinsa kuma harshen wuta, dukan ƙafafun kursiyin masu kama da keken yaƙin, wuta ne.
Ke nga ngetang liye ma inge, oasr kutu nien muta fulat oakwuki in acn sac. Sie su nuna moul oemeet me el muta fin sie mwe muta inge. Nuknuk lal uh fasrfasr oana snow, ac aunsifal nasnas oana unen sheep. Mwe muta se lal inge oan fin wheel ma firir, ac sarmelik oana e,
10 Kogin wuta yana gudu, yana fitowa daga gabansa. Dubun dubbai sun yi masa hidima; dubu goma sau dubu goma sun tsaya a gabansa. Aka zauna don shari’a, aka kuma buɗe littattafai.
ac soko koa in e uh sroma liki mwe muta fulat sac oana soko infacl. Oasr tausin puspis mwet su akola in kulansupwal, ac million puspis mwet tu ye mutal. Na nununku uh mutawauk, ac book uh ikakla.
11 “Sa’an nan na ci gaba da kallo saboda kalmomin fariyar da wannan ƙaho yake furtawa. Na yi ta kallo har sai da aka yanke dabbar, aka kuma hallaka jikinta a cikin wuta.
Ke nga ngetang liye ah, nga srakna lohng pusren tungak ac sifacna konkin lun koac srisrik soko ah. Nga srakna ngetang a kosro soko akakosr ah anwuki, ac manol sisiyang nu in e uh ac isisyak.
12 (An tuɓe sauran dabbobin daga mulkinsu, amma aka bar su su rayu na wani lokaci.)
Kosro saya ah itukla wal lalos, tusruktu filfilla elos in sifilpa muta ke kitin pacl.
13 “A wahayina na dare, na ga a gabana wani kamar ɗan mutum yana saukowa tare da gizagizan sama. Ya kusaci Wannan wanda yake Tun fil azal aka kuma kai shi gabansa.
Ke pacl se nga liye aruruma se inge in fong sac, nga liye sie ma su oana luman mwet se. El fahsru ac pukunyeng uh apnulla, na el fahla nu yurin el su moul oemeet me, ac kolyukla el nu ye mutal.
14 Aka ba shi mulki, daraja da kuma mafificin iko; dukan mutane, da al’ummai, da mutane daga kowane harshe suka yi masa sujada. Mulkinsa kuwa dawwammamen mulki ne da ba zai ƙare ba, sarautarsa kuma ba ta taɓa lalacewa.
Itukyang nu sel wal, sunak, ac ku fulat, tuh mwet in mutunfacl nukewa ac kain in kas nukewa fah kulansapwal. Ku fulat lal ac fah oan ma pahtpat, ac tokosrai lal ac fah wangin saflaiya.
15 “Ni, Daniyel, ruhuna ya damu ƙwarai, kuma wahayin da ya ratsa tunanina ya dame ni.
Aruruma ma nga liye inge oru nga fosrngala ac arulana fohsak.
16 Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda suke tsaye a can, na tambaye shi gaskiya ma’anar waɗannan al’amura. “Don haka sai ya faɗa mini, ya kuma ba ni fassarar waɗannan al’amura.
Nga fahsryang nu yurin sie selos su tu insac, ac siyuk lah el ac ku in akkalemye kalmen ma inge nu sik. Na el fahkma kalmac uh.
17 ‘Waɗannan manyan dabbobi huɗu, Masarautai ne huɗu waɗanda za su taso a duniya.
El fahk ouinge, “Kosro lulap akosr inge pa tokosrai lulap akosr ma ac sikyak fin faclu.
18 Amma tsarkaka na Mafi Ɗaukaka za su karɓi wannan sarauta, za su kuwa mallake ta har abada, I, har abada abadin.’
Ac mwet lun God Fulatlana elos ac fah eis ku fulat ac sruokya nwe tok ma pahtpat.”
19 “Sa’an nan kuma sai na so in san ma’anar wannan dabba ta huɗu, wadda ta yi dabam da sauran dabbobin da suke da matuƙar bantsoro, da take da haƙoran ƙarfe da kuma farcen tagulla, dabbar ta ragargaje ta cinye abin da ta kama, ta kuma tattaka duk abin da ya rage a ƙarƙashin ƙafafunta.
Ac nga sifilpa ke lohng kutu ke kosro soko akakosr ma tia oana kosro saya nufon — kosro aksangeng soko ma ac sang wihs osra kacl uh ac nia bronze kacl uh in itungya ma el sruokya uh, na lolongya.
20 Na kuma so in gane game da ƙahonin nan guda goma da suke a kanta da kuma game da ƙahon nan da ya fito, wanda aka tumɓuke ƙahoni uku a gabansa, ƙahon nan da yake da idanu da bakin da yake furta manyan maganganun fariya, wanda ya yi kamar ya fi sauran girma.
Ac nga ke etu pac ke koac singoul ke sifal, ac ke koac soko ma sikyak pac tok ac oru tolkwe koac uh in putatla ah. Oasr atronmutal ac oalul, ac arulana upa tungak lal uh. Yohk aksangeng lal uh liki koac nukewa saya ah.
21 Ina cikin dubawa, sai ga wannan ƙaho yana yaƙi da tsarkaka yana kuma cin nasara a kansu,
Ke nga ngetang liye ma inge, na koac srisrik soko ah mweun lain mwet lun God ac kutangulosla.
22 sai da Wannan wanda yake tun fil azal ya zo ya furta hukunci, aka kuma ba tsarkaka na Mafi Ɗaukaka gaskiya, lokaci kuwa ya cika sai suka karɓi mulki.
Na el su nuna moul oemeet me tuku, ac akkalemye lah nununku lal wi layen mwet lun God Fulatlana. Sun tari pacl fal tuh mwet lun God in eis ku fulat lun tokosra.
23 “Sai ya ba ni wannan bayani, ‘Dabbar nan ta huɗu, ita ce mulki na huɗu da zai bayyana a duniya. Zai bambanta da dukan sauran mulkoki, zai kuma cinye dukan duniya, yă tattake ta, yă kuma ragargaje ta.
Pa inge ma el aketeya nu sik: “Kosro soko akakosr ah pa tokosrai lulap se akakosr ma ac sikyak nu fin faclu, ac el ac fah siena liki tokosrai lulap nukewa saya uh. El ac fah itungya faclu nufon, ac futfutungya.
24 Ƙahonin nan goma, sarakuna ne goma waɗanda za su taso daga wannan mulki. Bayansu kuma, wani sarki zai taso, wanda ya sha dabam da waɗanda suka riga shi. Zai rinjayi sarakunan nan uku.
Koac singoul ah pa tokosra singoul ma ac leumi tokosrai lulap sac. Na sie pac tokosra ac fah sikyak, ac el ac arulana sie liki na tokosra nukewa ma tuku meet ah, ac el ac fah sinukunla tokosra tolu.
25 Zai yi maganar saɓo a kan Mafi Ɗaukaka, zai kuma tsananta wa tsarkaka yă kuma yi ƙoƙarin sāke lokuta da shari’u. Za a miƙa tsarkaka a hannunsa na wani lokaci, lokuta da kuma rabin lokaci.
El ac fah kaskas lain God Fulatlana, ac akkeokye mwet lun God. El ac fah srike elan ekulla ma sap lun lulalfongi lalos ac len in kufwa lalos, na mwet lun God uh ac fah muta ye ku lal ke lusen yac tolu tafu.
26 “‘Amma majalisa za tă yi zama, za a karɓe ikonsa, a kuma hallaka shi gaba ɗaya har abada.
Na nununku uh ac fah mutawauk, ac eisla ku lal uh, ac arulana kunausulla.
27 Sa’an nan za a ba da mulki, iko da girma na mulkokin da suke a ƙarƙashin dukan sammai ga tsarkaka, mutane na Mafi Ɗaukaka. Mulkinsa kuwa mulki ne marar matuƙa, kuma dukan masu mulki za su yabe shi, su kuma yi masa biyayya.’
Ku ac pwengpeng lun tokosrai nukewa fin faclu ac fah itukyang nu sin mwet lun God Fulatlana. Ku fulat lalos ac fah wangin saflaiya, ac mwet kol nukewa fin faclu ac fah kulansupwalos ac akos sap lalos.”
28 “Wannan shi ne ƙarshen batun. Ni, Daniyel na damu ƙwarai da irin tunanina, kuma fuskata ta rikice, amma na riƙe batun a zuciyata.”
Pa inge saflaiyen ma srumunyuk uh. Yoklana sangeng luk, oru nga arulana efla, ac nga sruokyana ma inge oan sik.

< Daniyel 7 >