< Amos 1 >

1 Kalmomin Amos, ɗaya daga cikin makiyayan Tekowa, abubuwan da ya gani game da Isra’ila shekaru biyu kafin a yi girgizar ƙasa, a lokacin da Uzziya yake sarkin Yahuda, Yerobowam ɗan Yowash kuma yake sarkin Isra’ila.
Words of Amos—who has been among herdsmen of Tekoa—that he has seen concerning Israel, in the days of Uzziah king of Judah, and in the days of Jeroboam son of Joash king of Israel, two years before the shaking;
2 Ya ce, “Ubangiji ya yi ruri daga Sihiyona ya kuma yi tsawa daga Urushalima; wuraren kiwo duk sun bushe, dutsen Karmel kuma ya yi yaushi.”
and he says, “YHWH roars from Zion, And gives forth His voice from Jerusalem, And pastures of the shepherds have mourned, And the top of Carmel has withered!”
3 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Damaskus, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Domin sun ci zalunci Gileyad zalunci mai tsanani,
And thus said YHWH: “For three transgressions of Damascus, And for four, I do not reverse it, Because of their threshing Gilead with sharp-pointed irons,
4 zan sa wuta a gidan Hazayel, da za tă ƙona kagarun Ben-Hadad.
And I have sent a fire against the house of Hazael, And it has consumed the palaces of Ben-Hadad.
5 Zan kakkarye ƙofofin Bet-Damaskus; zan hallaka sarkin da yake cikin Kwarin Awen da kuma mai riƙe da sandar mulkin Bet-Eden. Mutanen Aram za su je bauta a ƙasar Kir,” in ji Ubangiji.
And I have broken the bar of Damascus, And cut off the inhabitant from Bikat-Aven, And a holder of a scepter from Beth-Eden, And the people of Aram have been removed to Kir,” said YHWH.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Gaza, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun sayar wa Edom,
Thus said YHWH: “For three transgressions of Gaza, And for four, I do not reverse it, Because of their removing a complete captivity, To deliver up to Edom,
7 Zan aika da wuta a katangar Gaza ta ƙone duk kagarunta.
And I have sent a fire against the wall of Gaza, And it has consumed her palaces;
8 Zan hallaka sarkin Ashdod da kuma mai riƙe da sandar mulki na Ashkelon. Zan hukunta Ekron, har sai dukan Filistiyawa sun mutu,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And I have cut off the inhabitant from Ashdod, And a holder of a scepter from Ashkelon, And have turned back My hand against Ekron, And the remnant of the Philistines have perished,” said Lord YHWH.
9 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Taya, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun kwashe al’umma gaba ɗaya sun kai su bauta a Edom, ba su kula da yarjejjeniyar da aka yi ta zama kamar’yan’uwa ba,
Thus said YHWH: “For three transgressions of Tyre, And for four, I do not reverse it, Because of their delivering up a complete captivity to Edom, And they did not remember the brotherly covenant,
10 zan aika da wuta a Taya, da za tă ƙone kagarunta.”
And I have sent a fire against the wall of Tyre, And it has consumed her palaces.”
11 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Edom, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya fafari ɗan’uwansa da takobi, babu tausayi, domin ya ci gaba da fusata bai yarda yă huce daga fushinsa ba.
Thus said YHWH: “For three transgressions of Edom, And for four, I do not reverse it, Because of his pursuing his brother with a sword, And he has destroyed his mercies, And his anger tears continuously, And his wrath—he has kept it forever,
12 Zan aika wuta a Teman da za tă ƙone kagarun Bozra.”
And I have sent a fire against Teman, And it has consumed palaces of Bozrah.”
13 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Ammon, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta shi ba. Don ya tsaga cikin matan Gileyad masu juna biyu don kawai yă ƙwace ƙasar.
Thus said YHWH: “For three transgressions of the sons of Ammon, And for four, I do not reverse it, Because of their ripping up the pregnant ones of Gilead, To enlarge their border,
14 Zan sa wuta a katangar Rabba da za tă ƙone kagarunta za a yi kururuwa a ranar yaƙi, faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri.
And I have kindled a fire against the wall of Rabbah, And it has consumed her palaces, With a shout in a day of battle, With a whirlwind in a day of windstorm,
15 Sarkinta zai je bauta, shi da ma’aikatansa,” in ji Ubangiji.
And their king has gone in a removal, He and his heads together,” said YHWH!

< Amos 1 >