< Amos 5 >

1 Ku ji wannan magana, ya gidan Isra’ila, ina makokin nan dominku.
Ouvi esta palavra, que levanto sobre vós uma lamentação, ó casa de Israel.
2 “Budurwa Isra’ila ta fāɗi, ba za tă ƙara tashi ba, an yashe ta a ƙasarta, ba wanda zai ɗaga ta.”
A virgem de Israel caiu, nunca mais tornará a levantar-se: desamparada está na sua terra, não ha quem a levante.
3 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Birnin da ta fitar da masu ƙarfi dubbai don Isra’ila guda ɗari kaɗai za su dawo; garin da ya fitar da masu ƙarfi ɗari kuwa goma kaɗai za su dawo.”
Porque assim diz o Senhor Jehovah: A cidade da qual saem mil conservará cem, e aquella da qual saem cem conservará dez á casa de Israel.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce wa gidan Isra’ila. “Ku neme ni ku rayu;
Porque assim diz o Senhor á casa de Israel: Buscae-me, e vivei.
5 kada ku nemi Betel, kada ku je Gilgal, kada ku yi tafiya zuwa Beyersheba. Gama ba shakka Gilgal za tă tafi bauta, za a kuwa mai da Betel ba kome ba.”
Porém não busqueis a Beth-el, nem venhaes a Gilgal, nem passeis a Berseba, porque Gilgal certamente será levado captivo, e Beth-el será desfeito em nada.
6 Ku nemi Ubangiji ku kuma rayu, ko kuwa zai ratsa yă share gidan Yusuf kamar wuta; zai cinye Betel kuwa ba zai sami wanda zai kashe ta ba.
Buscae ao Senhor, e vivei, para que não accommetta a casa de José como um fogo, e a consuma, e não haja em Beth-el quem o apague.
7 Ku ne masu mai da gaskiya ta koma ɗaci ku kuma zubar da adalci.
(Os que pervertem o juizo em alosna, e deitam na terra a justiça.)
8 (Shi wanda ya yi Taurarin nan da ake ce Kaza da’Ya’yanta da kuma Mai Farauta da Kare, wanda ya mai da duhu ya zama haske ya kuma baƙanta rana ta zama dare, yakan kwashe ruwan teku ya zubar a ƙasa, Ubangiji ne sunansa,
O que faz o setestrello, e o orion, e torna a sombra da noite em manhã, e escurece o dia como a noite, que chama as aguas do mar, e as derrama sobre a terra, o Senhor é o seu nome.
9 yakan kawo hallaka a mafaka mai ƙarfi yakan kuma mai da birnin mai katanga ya zama kufai).
O que esforça o despojado contra o forte: assim que venha a assolação contra a fortaleza.
10 Ba ku son mai yin gaskiya a ɗakin shari’a kuna ƙin mai faɗar gaskiya.
Na porta aborrecem o que os reprehende, e abominam o que falla sinceramente.
11 Kuna matsa wa matalauta kuna sa su dole su ba ku hatsi. Saboda haka, ko da yake kun gina gidajen duwatsu, ba za ku zauna a cikinsu ba; ko da yake kun nome gonaki masu kyau, ba za ku sha ruwan inabinsu ba.
Portanto, visto que pizaes o pobre, e d'elle tomaes um cargo de trigo, edificastes casas de pedras lavradas, mas n'ellas não habitareis; vinhas desejaveis plantastes, mas não bebereis do seu vinho.
12 Gama na san yawan laifofinku da kuma girman zunubanku. Kuna danne masu adalci kuna kuma cin hanci kuna kuma hana a yi wa matalauta shari’ar adalci a majalisa.
Porque sei que são muitas as vossas transgressões, e grossos os vossos peccados: affligem o justo, tomam resgate, e rejeitam os necessitados na porta.
13 Saboda haka mai hankali yakan yi shiru a lokuta kamar haka, gama lokutan mugaye ne.
Portanto, o prudente n'aquelle tempo se calará, porque o tempo será mau.
14 Ku yi nagarta, ba mugunta ba; don ku rayu sa’an nan Ubangiji Allah Maɗaukaki zai kasance da ku, kamar yadda kuka ce zai yi.
Buscae o bem, e não o mal, para que vivaes: e assim o Senhor, o Deus dos Exercitos, estará comvosco, como dizeis.
15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta; ku dinga yin shari’ar gaskiya a ɗakunan shari’a. Mai yiwuwa Ubangiji Allah Maɗaukaki zai ji tausayin raguwar Yusuf.
Aborrecei o mal, e amae o bem, e estabelecei o juizo na porta: porventura o Senhor, o Deus dos Exercitos, terá piedade do resto de José.
16 Saboda haka ga abin da Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki yana cewa, “Za a yi kururuwa a dukan tituna a kuma yi kuka don azaba a dukan wuraren da jama’a sukan taru. Za a yi kira ga manoma su yi kuka masu makoki kuma su yi kuka.
Portanto, assim diz o Senhor Deus dos Exercitos, o Senhor: Em todas as ruas haverá pranto, e em todos os bairros dirão: Ai! ai! E ao lavrador chamarão a choro, e ao pranto aos que souberem prantear.
17 Za a yi kuka a dukan gonakin inabi, gama zan ratsa a cikinku,” in ji Ubangiji.
E em todas as vinhas haverá pranto; porque passarei pelo meio de ti, diz o Senhor.
18 Kaitonku masu son ganin ranar Ubangiji! Don me kuke son ganin ranar Ubangiji? Za a duhunta ranan nan, ba haske ba.
Ai d'aquelles que desejam o dia do Senhor! para que pois vos será este dia do Senhor? trevas será e não luz.
19 Za ku zama kamar mutanen da suka guje wa zaki sai suka fāɗa a hannun beyar, ko kuma kamar wanda ya shiga gida ya dāfa hannu a bango sai maciji ya sare shi.
Como o que foge de diante do leão, e se encontra com elle o urso, ou como se entrasse n'uma casa, e a sua mão encostasse á parede, e fosse mordido d'uma cobra.
20 Ashe, ranar Ubangiji ba duhu ba ce, a maimakon haske, duhu wuluk, ba tare da ko ɗan haske ba.
Não será pois o dia do Senhor trevas e não luz? e escuridade, sem que haja resplandor?
21 “Na ƙi, ina kuma ƙyamar bukukkuwanku na addini; ba na son ganin tarurrukanku.
Aborreço, desprezo as vossas festas, e os vossos dias de prohibição não me darão bom cheiro.
22 Ko da kun kawo mini hadayu na ƙonawa da kuma hadayu na hatsi, ba zan karɓa ba. Ko da kun kawo zaɓaɓɓun hadayu na zumunta, ba zan ɗauke su a bakin kome ba.
Porque ainda que me offereceis holocaustos, como tambem as vossas offertas de manjares, não me agrado d'ellas: nem attentarei para as offertas pacificas de vossos animaes gordos.
23 Ku tashi daga nan da surutan waƙoƙinku! Ba zan saurari kaɗe-kaɗe da bushe bushenku ba.
Affasta de mim o estrepito dos teus canticos; porque não ouvirei as psalmodias dos teus instrumentos.
24 Amma bari gaskiya ta kwararo kamar kogi, adalci kuma kamar rafin da ba ya taɓa bushewa!
Corra porém o juizo como as aguas, e a justiça como o ribeiro impetuoso.
25 “Kun kawo mini hadayu da sadakoki shekaru arba’in a cikin jeji, ya ku gidan Isra’ila?
Haveis-me porventura offerecido sacrificios e offertas no deserto por quarenta annos, ó casa de Israel?
26 Kun ɗaga masujadar sarkinku, siffofin gumakanku, tauraron allahnku, wanda kuka yi wa kanku.
Antes levastes a tenda de vosso Moloch, e a estatua das vossas imagens, a estrella do vosso deus, que fizestes para vós mesmos.
27 Saboda haka zan tura ku zaman bauta gaba da Damaskus,” in ji Ubangiji, wanda sunansa ne Allah Mai Iko.
Portanto vos levarei captivos, para além de Damasco, diz o Senhor, cujo nome é o Deus dos exercitos.

< Amos 5 >