< Amos 3 >

1 Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
Ey İsrailliler, kulak verin RAB'bin size, Mısır'dan çıkardığı halka söylediği şu sözlere:
2 “Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
“Yeryüzündeki bütün halklar arasından yalnız sizi tanıdım, Bu yüzden suçlarınızı karşılıksız bırakmayacağım.”
3 Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
İki kişi anlaşmadan birlikte yürür mü?
4 Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
Avı olmayan aslan ormanda kükrer mi? Bir şey yakalamadıkça genç aslan ininde homurdanır mı?
5 Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
Tuzak kurulmamışsa, Yerdeki kapana kuş düşer mi? İçine bir şey düşmedikçe Kapan yerden fırlar mı?
6 Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
Kentte boru çalınır da halk korkmaz mı? RAB'bin onayı olmadan bir kentin başına felaket gelir mi?
7 Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
Gerçek şu ki, Egemen RAB kulu peygamberlere Sırrını açmadıkça bir şey yapmaz.
8 Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
Aslan kükrer de kim korkmaz? Egemen RAB söyler de kim peygamberlik etmez?
9 Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
Aşdot ve Mısır saraylarına duyurun: “Samiriye dağlarında toplanın” deyin, “Kentin ortasındaki büyük kargaşayı, İçindeki baskıyı görün.”
10 “Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
RAB, “Onlar doğruluk nedir bilmiyorlar” diyor, “Saraylarına zorbalık ve çapul yığmışlar.”
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
Bu yüzden Egemen RAB diyor ki, “Düşman kuşatmakta ülkenizi, Saraylarınızı yağmalayacak, güçsüz kılacak sizi.”
12 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
RAB şöyle diyor: “Bir çoban aslanın ağzındaki hayvanın iki bacağını Ya da kulağının parçasını nasıl kaparsa, Samiriye'de sedir köşelerine, Divan yastıklarına Kurulan İsrailliler de öyle kurtarılacak.
13 “Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Dinleyin ve Yakup soyunu uyarın.” Egemen RAB, Her Şeye Egemen Tanrı konuşuyor:
14 “A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
“İsyanlarından ötürü İsrail'i cezalandırdığım gün, Beytel'in sunaklarını da yok edeceğim. Kesilip yere düşecek sunağın boynuzları.
15 Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.
Hem kışlık hem yazlık evi vuracağım, Yok olacak fildişi evler, Sonu gelecek büyük evlerin.” RAB böyle diyor.

< Amos 3 >