< Amos 3 >

1 Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
Oíd esta palabra que Yahvé ha pronunciado acerca de vosotros, oh hijos de Israel, acerca de toda la familia que Yo saqué de la tierra de Egipto, diciendo:
2 “Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
“De todas las tribus de la tierra solo conocí a vosotros; por eso os visitaré por todas vuestras maldades.
3 Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
¿Pueden acaso dos ir juntos sin estar de acuerdo?
4 Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
¿Por ventura brama el león en el bosque si no tiene presa? ¿Alza su rugido el leoncillo desde su cubil si nada ha apresado?
5 Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
¿Caerá el pájaro en el lazo sobre la tierra, sin ponérsele cebo? ¿Quién levanta el lazo desde el suelo sin estar de acuerdo?
6 Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
¿Se toca acaso la trompeta en la ciudad sin que se estremezca el pueblo? ¿Habrá calamidad en alguna ciudad sin disposición de Yahvé?
7 Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
Pues Yahvé, el Señor, no hará nada sin revelar su secreto a sus siervos los profetas.
8 Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
Si ruge el león, ¿quién no temerá? Si habla Yahvé, el Señor, ¿quién no profetizará?
9 Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
Pregonadlo en los palacios de Azoto y en los palacios del país de Egipto, y decid: “Congregaos en los montes de Samaria, y ved la enorme inmoralidad en medio de ella, y las violencias que allí se cometen.”
10 “Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
No saben hacer lo justo, dice Yahvé; amontonan en sus palacios rapiña y robo.
11 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
Por lo cual, así dice Yahvé, el Señor: “El enemigo rodeará el país y te quitará tu fuerza, y saqueados serán tus palacios.”
12 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
Así dice Yahvé: “Como el pastor arranca de la boca del león dos patas o la punta de una oreja, así serán salvados los hijos de Israel que se hallan en Samaria, en el ángulo del diván o sobre un lecho damasquino.
13 “Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
Oíd y dad testimonio contra la casa de Jacob, dice Yahvé, el Señor, el Dios de los ejércitos.
14 “A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
Porque el día que Yo castigare las prevaricaciones de Israel, (lo) castigaré también por los altares de Betel, y serán rotos los cuernos del altar y caerán a tierra.
15 Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.
Destruiré las casas de invierno juntamente con las casas de verano; quedarán arrasados los palacios de marfil, y desaparecerán muchas casas”, dice Yahvé.

< Amos 3 >