< Amos 2 >
1 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
Detta säger Herren: För tre och fyra Moabs lasters skull, vill jag intet skona honom; derföre, att de hafva uppbränt Konungens ben i Edom till asko;
2 Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
Utan jag vill sända en eld i Moab; han skall förtära palatsen i Kerioth, och Moab skall dö uti buller, rop och basunsklang.
3 Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
Och jag skall borttaga domaren ifrå honom, och dräpa alla hans Förstar med honom, säger Herren.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
Detta säger Herren: För tre och fyra Juda lasters skull, vill jag intet skona honom; derföre, att de förakta Herrans lag, och icke hålla hans rätter, och låta sina lögn förföra sig, hvilka deras fäder efterföljt hafva,
5 Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
Utan jag vill sända en eld i Juda han skall förtära palatsen i Jerusalem.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
Detta säger Herren: För tre och fyra Israels lasters skull, vill jag intet skona honom; derföre, att de sälja de rättfärdiga för penningar, och de fattiga för ett par skor.
7 Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
De gå med fötterna öfver de fattiga, och hindra de elända allestäds; sonen och fadren sofva när ena qvinno, med hvilko de ohelga mitt Namn.
8 Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
Och vid all altare slösa de af förpantad kläder, och dricka vin i sins Guds huse af saköre.
9 “Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
Nu hafver jag dock förlagt Amoreen för dem, den så hög var som cedreträ, och hans magt såsom eker; och jag förderfvade hans frukt ofvantill, och bans rötter nedantill.
10 Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
Hafver jag ock fört eder utur Egypti land, och ledt eder uti öknene i fyratio år, att I de Amoreers land besitta skullen?
11 “Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
Och af edrom barnom uppväckt eder Propheter, och af edrom ynglingom Nazareer? Är det icke så, I Israels barn? säger Herren.
12 “Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
Så gåfven I de Nazareer dricka vin, och Prophetomen böden I, och saden: I skolen intet prophetera.
13 “Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
Si, jag vill göra ibland eder ett gnisslande, såsom en vagn full af kärfvar gnisslar;
14 Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
Att den der rask är, skall icke kunna undfly, ej heller den starke något förmå, och den mägtige skall icke kunna undsätta sitt lif;
15 ’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
Och de bågaskyttar skola icke bestå; och den der rask är till att löpa, skall icke undlöpa; och den der rider, skall icke rädda sitt lit;
16 Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.
Och den der aldramanligast är ibland de starka, måste i den tiden nakot undfly, säger Herren.