< Amos 2 >

1 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Mowab, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama ya ƙone ƙasusuwan sarkin Edom suka zama sai ka ce toka.
Yahvé dice: “Por tres transgresiones de Moab, sí, por cuatro, No rechazaré su castigo, porque quemó los huesos del rey de Edom hasta convertirlos en cal;
2 Zan sa wuta a Mowab da za tă ƙone kagarun Keriyot Mowab za tă gangara cikin hayaniya mai girma cikin kururuwar yaƙi da kuma ƙarar ƙaho.
pero enviaré un fuego sobre Moab, y devorará los palacios de Kerioth; y Moab morirá con tumulto, con gritos y con el sonido de la trompeta;
3 Zan hallaka mai mulkinta zan kuma kashe shugabanninta.”
y cortaré al juez de entre ellos, y matará a todos sus príncipes con él”. dice Yahvé.
4 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Yahuda, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Gama sun ƙi bin dokar Ubangiji ba su kuma yi biyayya da ƙa’idodinsa ba, domin allolin ƙarya sun ruɗe su, allolin da kakanninsu suka bauta.
Yahvé dice: “Por tres transgresiones de Judá, sí, por cuatro, No rechazaré su castigo, porque han rechazado la ley de Yahvé, y no han guardado sus estatutos, y sus mentiras los han llevado por el mal camino, tras la cual caminaron sus padres;
5 Zan sa wuta a Yahuda da za tă ƙone kagarun Urushalima.”
pero enviaré un fuego sobre Judá, y devorará los palacios de Jerusalén”.
6 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Saboda zunubai uku na Isra’ila, har guda huɗu ma, ba zan fasa hukunta su ba. Don sun sayar da adalai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta waɗanda bashinsu bai ma kai ko kuɗin bi-labi ba.
Yahvé dice: “Por tres transgresiones de Israel, sí, por cuatro, No rechazaré su castigo, porque han vendido a los justos por plata, y a los necesitados por un par de sandalias;
7 Sun tattake kawunan matalauta kamar yadda suke taka laka suka kuma danne wa marasa galihu gaskiya. Uba da ɗa su na kwana da yarinya guda, suna kuma ɓata sunana mai tsarki.
Pisotean las cabezas de los pobres en el polvo de la tierra y negar la justicia a los oprimidos. Un hombre y su padre usan la misma doncella, para profanar mi santo nombre.
8 Suna kwanciya kurkusa da kowane bagade a kan tufafin da suka karɓe jingina. A gidajen allolinsu sukan sha ruwan inabin da suka karɓo daga wurin waɗanda suka ci wa tara.
Se acostaron junto a cada altar sobre ropas tomadas en prenda. En la casa de su Dios beben el vino de los multados.
9 “Na hallaka mutumin Amoriyawa a gabansu, ko da yake ya yi dogo kamar itacen al’ul kuma mai ƙarfi kamar itacen oak. Na hallaka’ya’yan itatuwansa daga sama, da kuma jijiyoyinsa daga ƙasa.
Sin embargo, yo destruí al amorreo ante ellos, cuya altura era como la de los cedros, y era fuerte como los robles; sin embargo, destruí su fruto desde arriba, y sus raíces desde abajo.
10 Na fitar da ku daga ƙasar Masar, na kuma bishe ku tsawon shekaru arba’in a cikin hamada don in ba ku ƙasar Amoriyawa.
También te saqué de la tierra de Egipto y te condujo cuarenta años por el desierto, para poseer la tierra de los amorreos.
11 “Na kuma tā da annabawa daga cikin’ya’yanku maza waɗansu kuma su zama keɓaɓɓu daga cikin samarinku. Ba haka ba ne, mutanen Isra’ila?” In ji Ubangiji.
Yo levanté a algunos de tus hijos como profetas, y a algunos de sus jóvenes como nazireos. ¿No es esto cierto? ¿Israel, hijos de Israel?”, dice Yahvé.
12 “Amma kuka sa keɓaɓɓun suka sha ruwan inabi kuka kuma umarci annabawa kada su yi annabci.
“Pero tú les diste de beber vino a los nazireos, y ordenó a los profetas, diciendo: “¡No profeticen!
13 “Saboda haka, yanzu zan murƙushe ku kamar yadda amalanke yakan murƙushe sa’ad da aka yi masa labtun hatsi.
He aquí que te aplastaré en tu lugar, como aplasta un carro que está lleno de grano.
14 Masu gudu da sauri ba za su tsira ba, masu ƙarfi ba za su iya yin amfani da ƙarfinsu ba, jarumi kuma ba zai iya ceton ransa ba.
La huida perecerá de los veloces. El fuerte no fortalecerá su fuerza. El poderoso no se entregará.
15 ’Yan baka ba za su iya dāgewa ba, masu saurin gudu ba za su tsira ba mahayin dawakai kuma ba zai tsere da ransa ba.
El que maneja el arco no se sostiene. El que es rápido de pies no escapará. El que monta el caballo no se libra.
16 Ko jarumawa mafi jaruntaka za su gudu tsirara a ranan nan,” in ji Ubangiji.
El que es valiente entre los poderosos huirán desnudos ese día”. dice Yahvé.

< Amos 2 >