< 2 Sama’ila 3 >
1 Aka daɗe ana yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda. Dawuda kuwa ya yi ta ƙara ƙarfi, yayinda gidan Shawulu ya yi ta raguwa a ƙarfi.
Och det var ett långt örlig emellan Sauls hus och Davids hus; men David gick och förkofrades, och Sauls hus gick tillbaka och förminskades.
2 An haifa wa Dawuda’ya’ya maza a Hebron. Ɗansa na fari shi ne Amnon, ɗan Ahinowam mutuniyar Yezireyel;
Och David vordo födde bara i Hebron: hans förstfödde son Ammon, utaf Ahinoam den Jisreelitiskon;
3 na biyu shi ne Kileyab, ɗan Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel; na uku shi ne Absalom, ɗan Ma’aka’yar Talmai sarkin Geshur;
Den andre Chileab, utaf Abigail, Nabals hustru den Carmelitens; den tredje Absalom, Maachas son, Thalmai dotters, Konungens i Gesur;
4 na huɗu shi ne Adoniya, ɗan Haggit; na biyar shi ne Shefatiya, ɗan Abital;
Den fjerde Adonia, Haggiths son; den femte SephatJa, Abitals son;
5 na shida kuma shi ne Itireyam, ɗan Egla matar Dawuda. An haifi waɗannan wa Dawuda a Hebron.
Den sjette Jithream, utaf Egla, Davids hustru. Desse äro födde David i Hebron.
6 Sa’ad da ake yaƙi tsakanin gidan Shawulu da gidan Dawuda, sai Abner ya yi ta ƙarfafa matsayinsa a gidan Shawulu.
Som nu örlig var emellan Sauls hus och Davids hus, förstärkte Abner Sauls hus.
7 To, Shawulu yana da ƙwarƙwarar da ake kira Rizfa,’yar Aiya. Sai Ish-Boshet ya ce wa Abner, “Don me kake kwana da ƙwarƙwarar mahaifina?”
Och Saul hade ena frillo benämnd Rizpa, Aja dotter; och Isboseth sade till Abner: Hvi sofver du när mins faders frillo?
8 Abner ya husata saboda abin da Ish-Boshet ya ce, sai ya ce, “Kana tsammani ni mai cin amana ne? Kana zato ni mai goyon bayan Yahuda ne? Tun farko na nuna aminci ga gidan babanka Shawulu, da’yan’uwansa, da abokansa! Ban kuwa ba da kai a hannun Dawuda ba. Ga shi yanzu a kan mace za ka ga laifina?
Då vardt Abner ganska vred af denna Isboseths ord, och sade: Är jag då ett hundahufvud, jag som emot Juda gör barmhertighet på dins faders Sauls hus, och på hans bröder och vänner, och hafver icke gifvit dig i Davids händer; och du räknar mig i dag en ogerning till för en qvinnos skull?
9 Allah yă yi wa Abner hukunci mai tsanani, in ban goyi bayan Dawuda ya sami abin da Ubangiji ya yi masa alkawari da rantsuwa ba.
Gud göre med Abner det och det, om jag icke gör, såsom Herren David svorit hafver;
10 Zan kuma mayar wa Dawuda sarautar gidan Shawulu, in kafa kursiyin Dawuda a kan Isra’ila, da kan Yahuda tun daga Dan har zuwa Beyersheba.”
Att riket skall tagas ifrån Sauls hus; och Davids stol skall uppsätter varda öfver Israel och Juda, ifrå Dan allt intill BerSaba.
11 Ish-Boshet bai ƙara yin karambanin ce wa Abner kome ba, gama yana tsoronsa.
Och han kunde icke mer svara honom ett ord; ty han fruktade honom.
12 Sai Abner ya aiki manzanni a madadinsa wurin Dawuda su ce masa, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi yarjejjeniya da ni, zan kuwa taimake ka, in juye dukan Isra’ila zuwa ɓangarenka.”
Och Abner sände båd för sig till David, och lät säga honom: Hvem hörer landet till? Och sade: Gör ditt förbund med mig; si, min hand skall vara med dig, så att jag vill vända till dig hela Israel.
13 Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi yarjejjeniya da kai, amma fa ina bukata abu guda daga gare ka, kada ka zo gabana in ba tare da matata Mikal,’yar Shawulu ba.”
Han sade: Ja väl, jag vill göra förbund med dig; men ett beder jag af dig, att du icke ser mitt ansigte, förra än du förer till mig Michal, Sauls dotter, när du kommer till att se mitt ansigte.
14 Sai Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-Boshet ɗan Shawulu cewa, “Ka ba ni matata Mikal wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari na Filistiyawa.”
Sände ock David båd till Isboseth, Sauls son, och lät säga honom: Få mig mina hustru Michal, den jag mig fast hafver med hundrade Philisteers förhudar.
15 Sai Ish-Boshet ya ba da umarni, aka kuwa ɗauke ta daga gidan mijinta Faltiyel ɗan Layish.
Isboseth sände åstad, och lät taga henne ifrå mannen Phaltiel, Lais son.
16 Amma mijin ya raka ta, yana tafe yana kuka, ya bi ta har Bahurim. Sai Abner ya ce masa, “Koma gida!” Sai ya koma.
Och hennes man gick med henne, och gret efter henne, allt intill Bahurim. Då sade Abner till honom: Vänd om, och gack dina färde. Och han vände om igen.
17 Abner ya tattauna da dattawan Isra’ila ya ce, “An daɗe kuna nema ku naɗa Dawuda sarkinku.
Och Abner hade ett tal med de äldsta i Israel, och sade: I hafven länge tillförene åstundat David, att han måtte vara Konung öfver eder.
18 To, yanzu sai ku yi haka! Gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta wurin bawana Dawuda zan ceci mutanena Isra’ila daga hannun Filistiyawa, da kuma hannun dukan abokan gābansu.’”
Så görer ock så nu; förty Herren hafver sagt om David: Jag skall frälsa mitt folk Israel, genom min tjenares Davids hand, utu de Philisteers hand, och utur alla deras fiendars hand.
19 Abner kuma ya yi magana da mutane Benyamin da kansa. Sa’an nan ya tafi Hebron yă gaya wa Dawuda ko mene ne Isra’ila da kuma dukan gidan Benyamin suke so su yi.
Talade ock Abner för BenJamins öron; och gick desslikes bort till att tala för Davids öron i Hebron, allt det Israel och hela BenJamins hus täcktes.
20 Sa’ad da Abner wanda yake tare da mutane ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda ya shirya masa liyafa tare da mutanensa.
Då nu Abner kom till David i Hebron, och tjugu män med honom, gjorde David dem ett gästabåd.
21 Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Bari in tafi nan da nan in tattara dukan Isra’ila wa ranka yă daɗe, sarki, saboda su yi alkawari da kai, ka kuma ka yi mulki bisa dukansu yadda ranka yake so.” Saboda haka Dawuda ya sallami Abner, ya kuwa tafi lafiya.
Och Abner sade till David: Jag vill stå upp, och gå bort till att församla hela Israel till min herra Konungen, och att de skola göra ett förbund med dig; på det du må vara en Konung, såsom din själ det begärar. Så lät då David Abner gå ifrå sig med frid.
22 Ba a jima ba sai mutanen Dawuda da Yowab suka dawo daga hari. Suka kawo ganima da yawa tare da su. Abner kuwa ya riga ya bar Dawuda a Hebron, domin Dawuda ya sallame shi, shi kuma ya tafi lafiya.
Och si, Davids tjenare och Joab kommo ifrå krigsfolket, och hade ett stort rof med sig; men Abner var icke nu qvar när David i Hebron, utan han hade låtit honom ifrå sig, så att han med frid bortgången var.
23 Sa’ad da Yowab da dukan sojoji suka dawo, aka gaya masa cewa Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya sallame shi, ya kuma tafi lafiya.
Då nu Joab, och hela hären med honom, var kommen, vardt honom sagdt, att Abner, Ners son, var kommen till Konungen, och han hade låtit honom ifrå sig, så att han var med frid bortgången.
24 Sai Yowab ya je wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka. Don me ka ƙyale shi yă tafi? Ga shi kuwa ya tafi!
Så gick Joab in till Konungen, och sade: Hvad hafver du gjort? Si, Abner är kommen till dig: Hvi hafver du släppt honom ifrå dig, så att han är bortgången?
25 Ka san Abner ɗan Ner ya zo ne yă ruɗe ka, yă ga fitarka da shigarka, yă kuma binciki kome da kake yi.”
Känner du icke Abner, Ners son? Ty han är kommen till att bedraga dig, att han må bespeja din utgång och ingång, och få veta allt det du gör.
26 Yowab ya tashi daga gaban Dawuda ya tafi ya aika manzanni su bi Abner. Suka same shi a rijiyar Sira suka komo da shi, Dawuda kuwa bai sani ba.
Och som Joab utgick ifrån David, sände han båd efter Abner, att de skulle hem ta honom igen ifrå BorHasira; och David visste der intet af.
27 To, da Abner ya komo Hebron, Yowab ya ratse da shi zuwa hanyar shigar gari kamar zai gana da shi a kaɗaice. Amma a can ya soki Abner a ciki, ya kashe shi don yă rama mutuwar ɗan’uwansa Asahel.
Som nu Abner igenkom till Hebron, hade Joab honom midt uti porten, att han skulle tala med honom enskildt; och stack honom der i buken, så att han blef död, för hans broders Asahels blods skull.
28 Daga baya, Dawuda ya ji labarin sai ya ce, “Ni da masarautata har abada ba mu da laifi a gaban Ubangiji game da jinin Abner ɗan Ner.
När nu David detta hörde, sade han: Jag är oskyldig, och mitt rike, för Herranom evinnerliga, för Abners, Ners sons, blod;
29 Alhakin jininsa yă kasance a kan Yowab da kuma a kan dukan iyalin mahaifinsa! Kada gidan Yowab yă rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko mai jingina ga sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko kuma wanda ba shi da abinci.”
Men det komme öfver Joabs hufvud, och öfver hela hans faders hus; och vände icke åter i Joabs hus, den som en etterflöd och spitelsko hafver, och den som sländo håller, och den genom svärd faller och den som bröd fattas.
30 (Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka kashe Abner don yă kashe ɗan’uwansu Asahel a yaƙin Gibeyon.)
Alltså dråpo Joab och hans broder Abisai Abner, derföre att han slog deras broder Asahel ihjäl, i stridene vid Gibeon.
31 Sa’an nan Dawuda ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku yayyage rigunarku, ku sa tsummoki, ku yi tafiya kuna kuka a gaban Abner.” Sarki Dawuda kansa ya bi masu ɗauke da gawar daga baya.
Men David sade till Joab, och allt folket som med honom var: Rifver edor kläder sönder, och drager säcker uppå eder, och jämrer eder för Abners skull. Och Konungen gick efter bårena.
32 Suka binne Abner a Hebron, sarki kuwa ya ɗaga murya ya yi kuka a kabarin Abner.
Och då de begrofvo Abner i Hebron, upphof Konungen sina röst, och gret vid Abners graf; gret ock desslikes allt folket.
33 Sarki ya kuma yi wannan waƙar makoki domin Abner ya ce, “Daidai ne Abner yă mutu, kamar yadda marasa bin doka suke mutuwa?
Och Konungen beklagade sig öfver Abner, och sade: Abner är icke död såsom en dåre dör.
34 Hannuwanka ba a daure suke ba, ƙafafunka ba a tabaibaye suke ba. Ka mutu kamar waɗanda suke mutuwa a hannun mugaye.” Sai dukan mutane suka sāke fashe da kuka saboda shi.
Dina händer voro intet bundna; dina fötter voro intet satte i fjettrar; du äst fallen, såsom man faller för arga skalkar. Då begret folket honom än mer.
35 Sa’an nan duk suka zo suka roƙi Dawuda yă ci wani abu tun rana ba tă fāɗi ba; amma Dawuda ya rantse ya ce, “Bari Allah yă hukunta ni, in na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta fāɗi!”
Då nu allt folket kom in med David till att äta, och ännu bittida dags var, svor David, och sade: Gud göre mig det och det, om jag bröd eller något annat smakar, förrän solen nedergår.
36 Dukan mutane suka lura suka kuma ji daɗi ƙwarai, tabbatacce kome da sarki ya yi, ya gamshe su.
Och allt folket visste det, och det behagade dem väl allt det goda, som Konungen gjorde för hela folksens ögon.
37 Saboda haka a ranar dukan mutane da dukan Isra’ila suka gane sarki ba shi da hannu a kisan Abner ɗan Ner.
Och allt folket och hela Israel märkte på den dagen, att det var icke af Konungenom, att Abner, Ners son, vardt dräpen.
38 Sa’an nan sarki ya ce wa mutanensa, “Ba ku gane cewa ɗan sarki kuma babban mutum ya mutu a ƙasar Isra’ila a yau ba?
Och Konungen sade till sina tjenare: Veten I icke, att på denna dag är en Förste och stor man fallen i Israel?
39 A yau, ko da yake ni naɗaɗɗen sarki ne, duk da haka na raunana, kuma waɗannan’ya’yan Zeruhiya sun fi ƙarfina. Ubangiji yă sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata!”
Och jag är ännu späd, och en smord Konung; men de män ZeruJa söner äro mig allt för hårde; Herren vedergälle honom, som illa gör, efter hans ondsko.