< 2 Sama’ila 22 >

1 Dawuda ya rera wannan waƙa ga Ubangiji, sa’ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun dukan abokan gābansa, da kuma daga hannun Shawulu.
RAB, Davut'u bütün düşmanlarının ve Saul'un elinden kurtardığı gün Davut RAB'be şu ezgiyi okudu.
2 Ya ce, “Ubangiji shi ne dutsena, kagarata da kuma mai cetona;
Şöyle dedi: “RAB benim kayam, sığınağım, kurtarıcımdır,
3 Allahna shi ne dutsena. A gare shi nake samun kāriya shi ne garkuwata da kuma ƙahon cetona. Shi ne mafakata, maɓuyata, da mai cetona. Daga mutane masu fitina, ka cece ni.
Tanrım, kayamdır, O'na sığınırım, Kalkanım, güçlü kurtarıcım, Korunağım, sığınacak yerimdir. Kurtarıcım, zorbalıktan beni sen kurtarırsın!
4 “Na kira ga Ubangiji, wanda ya cancanci yabo, na kuwa tsira daga abokan gābana.
Övgüye değer RAB'be seslenir, Kurtulurum düşmanlarımdan.
5 Raƙumar ruwan mutuwa sun kewaye ni; raƙumar ruwan hallaka suna cin ƙarfina.
Çünkü ölüm dalgaları beni kuşattı, Yıkım selleri bastı,
6 Igiyoyin mutuwa sun nannaɗe ni; tarkuna kuma suka auka mini. (Sheol h7585)
Ölüler diyarının bağları sardı, Ölüm tuzakları çıktı karşıma. (Sheol h7585)
7 “A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji; na yi kira ga Allahna. Daga cikin haikalinsa ya saurare muryata; kukata ta zo kunnensa.
Sıkıntı içinde RAB'be yakardım, Tanrım'a seslendim. Tapınağından sesimi duydu, Haykırışım kulaklarına ulaştı.
8 Ƙasa ta yi rawa ta kuma girgiza, harsashan sararin sama sun jijjigu; suka yi makyarkyata saboda yana fushi.
O zaman yeryüzü sarsılıp sallandı, Titreyip sarsıldı göklerin temelleri, Çünkü RAB öfkelenmişti.
9 Hayaƙi ya taso daga kafaffen hancinsa; harshen wuta mai cinyewa daga bakinsa, garwashi mai ƙuna daga bakinsa.
Burnundan duman yükseldi, Ağzından kavurucu ateş Ve korlar fışkırdı.
10 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, girgije mai duhu suna ƙarƙashin ƙafafunsa.
Kara buluta basarak Gökleri yarıp indi.
11 Ya hau kerubobi, ya tashi sama; ya yi firiya a fikafikan iska.
Bir Keruv'a binip uçtu, Rüzgarın kanatları üstünde belirdi.
12 Ya mai da duhu abin rufuwarsa gizagizai masu kauri cike da ruwa suka kewaye shi.
Karanlığı örtündü, Kara bulutları kendine çardak yaptı.
13 Daga cikin hasken gabansa garwashi wuta mai ci ya yi walƙiya.
Varlığının parıltısından Korlar savruluyordu.
14 Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama; aka ji muryar Mafi Ɗaukaka.
RAB göklerden gürledi, Duyurdu sesini Yüceler Yücesi.
15 Ya harbe kibiyoyi, ya wartsar da abokan gāba, da walƙiya kuma ya sa suka gudu.
Savurup oklarını düşmanlarını dağıttı, Şimşek çaktırarak onları şaşkına çevirdi.
16 Aka bayyana kwarin teku, tushen duniya suka tonu. A tsawatawar Ubangiji, da numfashinsa mai ƙarfi daga hancinsa.
RAB'bin azarlamasından, Burnundan çıkan güçlü soluktan, Denizin dibi göründü, Yeryüzünün temelleri açığa çıktı.
17 “Daga sama ya miƙo hannu ya ɗauke ni, ya tsamo ni daga zurfafa ruwaye.
RAB yukarıdan elini uzatıp tuttu, Çıkardı beni derin sulardan.
18 Ya kuɓutar da ni daga hannun abokin gāba mai iko, daga maƙiyina da suka fi ƙarfina.
Beni zorlu düşmanımdan, Benden nefret edenlerden kurtardı, Çünkü onlar benden daha güçlüydü.
19 Suka auka mini cikin ranar masifata, amma Ubangiji ya kiyaye ni.
Felaket günümde karşıma dikildiler, Ama RAB bana destek oldu.
20 Ya fito da ni, ya kai ni wuri mafi fāɗi; ya kuɓutar da ni gama yana jin daɗina.
Beni huzura kavuşturdu, Kurtardı, çünkü benden hoşnut kaldı.
21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina; bisa ga tsabtar hannuwana ya sāka mini.
RAB doğruluğumun karşılığını verdi, Beni temiz ellerime göre ödüllendirdi.
22 Gama na kiyaye hanyoyin Ubangiji; ban yi wani mugun abu da zai juyar da ni daga Allahna ba.
Çünkü RAB'bin yolunda yürüdüm, Tanrım'dan uzaklaşarak kötülük yapmadım.
23 Dukan dokokinsa suna a gabana; ban ƙi ko ɗaya daga umarnansa ba.
O'nun bütün ilkelerini göz önünde tuttum, Kurallarından ayrılmadım.
24 Ba ni da laifi a gabansa na kiyaye kaina daga yin zunubi.
O'nun önünde kusursuzdum, Suç işlemekten sakındım.
25 Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina bisa ga tsarkina a gabansa.
Bu yüzden RAB beni doğruluğuma Ve gözünde pak yaşayışıma göre ödüllendirdi.
26 “Ga masu aminci, kakan nuna kanka mai aminci, ga marasa laifi, kakan nuna kanka marar laifi,
Sadık kuluna sadakat gösterir, Kusursuz olana kusursuz davranırsın.
27 ga masu tsarki, kakan nuna musu tsarki. Amma ga masu karkataccen hali, kakan nuna kanka mai wayo.
Pak olanla pak olur, Eğriye eğri davranırsın.
28 Kakan ceci mai tawali’u, amma idanunka suna a kan masu girman kai don ka ƙasƙantar da su.
Alçakgönüllüleri kurtarır, Gururluları gözler, gururunu kırarsın.
29 Ya Ubangiji kai ne fitilata; Ubangiji ya mai da duhuna haske.
Ya RAB, ışığım sensin! Karanlığımı aydınlatırsın.
30 Da taimakonka zan iya auka wa rundunar sojoji; tare da Allahna zan iya hawan katanga.
Desteğinle akıncılara saldırır, Seninle surları aşarım, Tanrım.
31 “Ga Allah dai, hanyarsa cikakkiya ce; maganar Ubangiji babu kuskure. Shi garkuwa ce ga waɗanda suka nemi mafaka a gare shi.
Tanrı'nın yolu kusursuzdur, RAB'bin sözü arıdır. O kendisine sığınan herkesin kalkanıdır.
32 Gama wane ne Allah, in ba Ubangiji ba? Wane ne dutse kuma in ba Allahnmu ba?
Var mı RAB'den başka tanrı? Tanrımız'dan başka kaya var mı?
33 Allah ne ya ba ni ƙarfi, ya kuma mai da hanyata cikakkiya.
Sığınağım Tanrı'dır, Yolumu doğru kılan O'dur.
34 Ya sa ƙafafuna kamar ƙafafun barewa; ya sa na iya tsayawa a kan duwatsu.
Ayaklar verdi bana, geyiklerinki gibi, Doruklarda tutar beni.
35 Ya hori hannuwana don yaƙi, hannuwana za su iya tanƙware bakan tagulla.
Bana savaşmayı öğretti, Kollarımla tunç bir yayı gereyim diye.
36 Ka ba ni garkuwar nasararka; ka sauko don ka sa in sami girma.
Bana zafer kalkanını bağışlarsın, Alçakgönüllülüğün beni yüceltir.
37 Ka fadada hanya a ƙarƙashina domin kada idon ƙafana yă juya.
Bastığım yerleri genişletirsin, Burkulmaz bileklerim.
38 “Na fafari abokan gābana, na murƙushe su; ban kuwa juya ba sai da na hallaka su.
Düşmanlarımı kovalayıp yok ettim, Hepsi yok olmadan geri dönmedim.
39 Na hallaka su ƙaƙaf, ba kuwa za su ƙara tashi ba, sun fāɗi a ƙarƙashin sawuna.
Onları ezip yok ettim, kalkamaz oldular, Ayaklarımın altına serildiler.
40 Ka ba ni ƙarfi don yaƙi; ka sa maƙiyina suka rusuna a ƙafafuna.
Savaş için beni güçle donattın, Bana başkaldıranları önümde yere serdin.
41 Ka sa abokan gābana suka juya a guje, na kuwa hallaka maƙiyina.
Düşmanlarımı kaçmak zorunda bıraktın, Benden nefret edenleri yok ettim.
42 Suka nemi taimako, amma babu wanda zai cece su, suka yi kira ga Ubangiji, amma ba a amsa musu ba.
Feryat ettiler, ama kurtaran çıkmadı; RAB'bi çağırdılar, ama O yanıt vermedi.
43 Na murƙushe su, suka yi laushi kamar ƙura; na daka na kuma tattake su kamar caɓi a kan tituna.
Yerin tozu gibi onları ezdim, Sokak çamuru gibi ayağımın altında çiğnedim.
44 “Ka kuɓutar da ni daga harin mutanena; ka kiyaye ni kamar shugaban al’ummai. Mutanen da ban sansu ba za su kasance a ƙarƙashina,
Halkımın çekişmelerinden beni kurtardın, Uluslara önder olarak beni korudun, Tanımadığım halklar bana kulluk ediyor.
45 baƙi kuma su na zuwa don su yi mini fadanci; da zarar sun ji ni, sukan yi mini biyayya.
Yabancılar bana boyun eğiyor, Duyar duymaz sözümü dinliyorlar.
46 Zukatansu ta karaya; suka fito da rawan jiki daga kagararsu.
Yabancıların betleri benizleri attı, Titreyerek çıkıyorlar kalelerinden.
47 “Ubangiji yana a raye! Yabo ta tabbata ga Dutsena! Ɗaukaka ga Allah, Dutse, Mai Cetona!
RAB yaşıyor! Kayam'a övgüler olsun! Yücelsin kurtarıcım, Kayam Tanrım!
48 Shi ne Allahn da yake rama mini, wanda ya sa al’ummai a ƙarƙashina,
O'dur öcümü alan, Halkları bana bağımlı kılan.
49 wanda ya kuɓutar da ni daga maƙiyina. Ka ɗaukaka ni bisa maƙiyina; ka kiyaye ni daga hannun mugayen mutane.
Düşmanlarımdan kurtarır, Başkaldıranlardan üstün kılar beni, Zorbaların elinden alır.
50 Saboda haka, zan yabe ka, ya Ubangiji cikin dukan al’ummai; Zan rera waƙoƙin yabo ga sunanka.
Bunun için uluslar arasında sana şükredeceğim, ya RAB, Adını ilahilerle öveceğim.
51 “Ya ba wa sarkinsa kyakkyawan nasara; ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shafaffensa, ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”
RAB kralını büyük zaferlere ulaştırır, Meshettiği krala, Davut'a ve soyuna Sonsuza dek sevgi gösterir.”

< 2 Sama’ila 22 >